ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 18, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

by Yusuf Shuaibu
3 weeks ago
makarfi

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Ahmed Mohammed Makarfi, ya musanta iƙirarin cewa za a iya yin maguɗin zaɓen babban zaɓen 2027, yana mai cewa irin waɗannan kalamai halayen ƴan siyasa ne da ba sa son yin aikin wahala da ake buƙata don cin zaɓe.

A cikin wata hira da ƴan jarida, Makarfi ya ce ya kamata ƴan siyasa su mayar da hankali wajen samun magoyon baya da ƙarfafa tsarin jam’iyyunsu, da kare sahihancin tsarin zaɓe maimakon yin zargin cewa ana shirin yin maguɗi tun da wuri.

Da yake mayar da martani kan damuwar da ake nunawa a wasu sassa cewa zaɓen gaba zai iya samun matsala, tsohon gwamnan ya ce ƴan siyasar da ke yin hasashen maguɗin zaɓe tun kafin a fara kaɗa ƙuri’a kawai suna neman uzuri ne.

ADVERTISEMENT

“Kawai wannan tunanin mutum mai kasala ne, tun daga farko, zai ce za a yi maguɗin zaɓe a 2027.

“Me ya sa za ka tashi ka bar zaɓe? Ka yi aiki don ka ci zaɓe, ka yi aiki don ka hana maguɗi, amma me ya sa za ka riƙa cewa abubuwa ba za su yi daidai ba? A’a, abubuwa suna daidai, sai dai idan mu muka bari su zama ba daidai ba,” in ji Makarfi.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Makarfi ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da ake ƙara samun haɗakar siyasa gabanin zaɓen 2027, inda jam’iyyun adawa da masu ruwa da tsaki ke nuna damuwa kan yadda za a gudanar da zaɓen.

Tsohon shugaban kwamitin riƙo na jam’iyyar PDP ya bayyana cewa maimakon haifar da tsoro da rashin yarda a tsarin zaɓe, ya kamata jam’iyyun siyasa su mai da hankali kan tsayar da nagartattun ƴan takara da kuma shawo kan ƴan Nijeriya su mara musu baya.

Ya kuma jaddada cewa dimokiraɗiyya tana bunƙasa ne idan ƴan siyasa suna shiga zaɓe cikin tsari da gaskiya maimakon yin hasashe kan sakamakon tun kafin a fara yaƙin neman zaɓe.

Game da halin da PDP ke ciki, Makarfi ya nuna kwarin gwiwa cewa jam’iyyar na da karfin gaske duk da ƙalubalen da take fuskanta.

“Tabbas, daga cikin dukkan jam’iyyun siyasa, ina ganin PDP, saboda tana da tushe mai ƙarfi kuma ba ta dogara da mutum guda ba, tana da makoma mai kyau.”

Sai dai ya amince cewa jam’iyyar ta fuskanci matsaloli kuma mambobinta sun samu rarrabuwan wajen kaɗa ƙuri’a a zaɓen shugaban ƙasa na baya, abin da ya ce yana nuna gaskiyar siyasa ta lokacin.

A cewarsa, zaɓe yana shafar abubuwa da dama, ciki har da biyayya ga jam’iyya, ƙabila, addini, cancantar ɗan takara da kuma yanayin da ake ciki.

“Wasu mutane za su zaɓa ne saboda jam’iyya. Wasu saboda addini ko ƙabila. Wasu kuma kawai saboda ba sa son wani,” in ji shi.

Makarfi ya ce babu wani ɗan takara ko jam’iyya da ya kamata ya ɗauka cewa nasara ta tabbata tun kafin zaɓen 2027, yana mai gargaɗin cewa ƴan Nijeriya suna ƙara wayewa wajen zaɓar shugabanni.

“Waɗanda ke cikin takara suna da aiki mai yawa a gabansu. Duk wanda yake tunanin zai zauna kawai nasara ta riga ta tabbata, yana raina hankalin ƴan Nijeriya,” in ji shi.

Tsohon gwamnan ya kuma sake jaddada cewa dole ne jam’iyyun siyasa su bi dokokin zaɓe da ƙa’idoji yayin fafutukar siyasa, yana mai cewa mutunta doka na da matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa tsarin dimokiraɗiyyar Nijeriya.

makarfi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

MASU ALAKA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
Fahimtar “Karin Damar Sin” Bisa Tsarin “Amfani Da Kirkire-Kirkire A Mabambantan Bangarori” Na Sin

Fahimtar "Karin Damar Sin" Bisa Tsarin "Amfani Da Kirkire-Kirkire A Mabambantan Bangarori" Na Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

Sin Za Ta Inganta Kaddamar Da Aikin Kungiyar Hadin Gwiwar AI Ta Duniya Da Wuri

July 17, 2026
Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

Sin Ta Yaba Da Matakin Amurka Na Kin Tsawaita Dokar Ta-Baci Dangane Da HK

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

Xi Ya Gana Da Babban Sakataren MDD Da Firaministocin Thailand Da CambodiaA

July 17, 2026
Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

Zaben Fidda Gwani Da Ake Takaddama:APC Ta Dauki Matakan Kauce Wa Shari’o’in Kotu

July 17, 2026
Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

Sin Ta Mika Sabuwar Manhajar Gargadin Gaggawa Ta MAZU Ga Djibouti

July 17, 2026
Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima

July 17, 2026
Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

Kwamitin Ba Da Shawara Kan Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Na Dandalin BRI Ya Yi Taronsa Na 2026

July 17, 2026
Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

Wang Huning Ya Ziyarci Koriya Ta Arewa

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.