ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 26, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

by Yusuf Shuaibu
2 hours ago
makarfi

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Ahmed Mohammed Makarfi, ya musanta iƙirarin cewa za a iya yin maguɗin zaɓen babban zaɓen 2027, yana mai cewa irin waɗannan kalamai halayen ƴan siyasa ne da ba sa son yin aikin wahala da ake buƙata don cin zaɓe.

A cikin wata hira da ƴan jarida, Makarfi ya ce ya kamata ƴan siyasa su mayar da hankali wajen samun magoyon baya da ƙarfafa tsarin jam’iyyunsu, da kare sahihancin tsarin zaɓe maimakon yin zargin cewa ana shirin yin maguɗi tun da wuri.

Da yake mayar da martani kan damuwar da ake nunawa a wasu sassa cewa zaɓen gaba zai iya samun matsala, tsohon gwamnan ya ce ƴan siyasar da ke yin hasashen maguɗin zaɓe tun kafin a fara kaɗa ƙuri’a kawai suna neman uzuri ne.

ADVERTISEMENT

“Kawai wannan tunanin mutum mai kasala ne, tun daga farko, zai ce za a yi maguɗin zaɓe a 2027.

“Me ya sa za ka tashi ka bar zaɓe? Ka yi aiki don ka ci zaɓe, ka yi aiki don ka hana maguɗi, amma me ya sa za ka riƙa cewa abubuwa ba za su yi daidai ba? A’a, abubuwa suna daidai, sai dai idan mu muka bari su zama ba daidai ba,” in ji Makarfi.

LABARAI MASU NASABA

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Makarfi ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da ake ƙara samun haɗakar siyasa gabanin zaɓen 2027, inda jam’iyyun adawa da masu ruwa da tsaki ke nuna damuwa kan yadda za a gudanar da zaɓen.

Tsohon shugaban kwamitin riƙo na jam’iyyar PDP ya bayyana cewa maimakon haifar da tsoro da rashin yarda a tsarin zaɓe, ya kamata jam’iyyun siyasa su mai da hankali kan tsayar da nagartattun ƴan takara da kuma shawo kan ƴan Nijeriya su mara musu baya.

Ya kuma jaddada cewa dimokiraɗiyya tana bunƙasa ne idan ƴan siyasa suna shiga zaɓe cikin tsari da gaskiya maimakon yin hasashe kan sakamakon tun kafin a fara yaƙin neman zaɓe.

Game da halin da PDP ke ciki, Makarfi ya nuna kwarin gwiwa cewa jam’iyyar na da karfin gaske duk da ƙalubalen da take fuskanta.

“Tabbas, daga cikin dukkan jam’iyyun siyasa, ina ganin PDP, saboda tana da tushe mai ƙarfi kuma ba ta dogara da mutum guda ba, tana da makoma mai kyau.”

Sai dai ya amince cewa jam’iyyar ta fuskanci matsaloli kuma mambobinta sun samu rarrabuwan wajen kaɗa ƙuri’a a zaɓen shugaban ƙasa na baya, abin da ya ce yana nuna gaskiyar siyasa ta lokacin.

A cewarsa, zaɓe yana shafar abubuwa da dama, ciki har da biyayya ga jam’iyya, ƙabila, addini, cancantar ɗan takara da kuma yanayin da ake ciki.

“Wasu mutane za su zaɓa ne saboda jam’iyya. Wasu saboda addini ko ƙabila. Wasu kuma kawai saboda ba sa son wani,” in ji shi.

Makarfi ya ce babu wani ɗan takara ko jam’iyya da ya kamata ya ɗauka cewa nasara ta tabbata tun kafin zaɓen 2027, yana mai gargaɗin cewa ƴan Nijeriya suna ƙara wayewa wajen zaɓar shugabanni.

“Waɗanda ke cikin takara suna da aiki mai yawa a gabansu. Duk wanda yake tunanin zai zauna kawai nasara ta riga ta tabbata, yana raina hankalin ƴan Nijeriya,” in ji shi.

Tsohon gwamnan ya kuma sake jaddada cewa dole ne jam’iyyun siyasa su bi dokokin zaɓe da ƙa’idoji yayin fafutukar siyasa, yana mai cewa mutunta doka na da matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa tsarin dimokiraɗiyyar Nijeriya.

makarfi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Next Post
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya, Bankin Duniya Da Cibiyar IITA Za Su Bunkasa Noma Ta Fasahar Zamani

Bankin Duniya Ya Ɗora Tashoshin Apapa Da Tincan Kan Sikelin Maki Na 20 A Duniya

June 26, 2026
sikila

Buƙatar Mayar Da Hankali Wajen Kawo Ƙarshen Ciwon Sikila A Nijeriya

June 26, 2026
Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

Sin Ta Bankado Laifukan Miyagun Kwayoyi 12,000 A Watanni Biyar Na Farkon Bana

June 26, 2026
makarfi

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

Kotu Ta Soke Rajistar Jam’iyyar NDC A Matsayin Jam’iyyar Siyasa

June 26, 2026
An Kashe Mutane Da Dama Da Kone Gidajensu A Wani Hari Da Aka Kai Benuwai

Yadda Rikice-rikice Ke Ƙara Ta’azzara Talauci A Arewacin Nijeriya —Rahoto

June 26, 2026
Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

Za A Sake Nazarin Mafi Ƙarancin Albashi A Nijeriya – Gbajabiamila

June 26, 2026
Sowore Ya Sha Alwashin Ci Gaba Da Gwagwarmaya Duk Da Tsare Shi A Gidan Yarin Kuje

Jagoran Matasan AAC Kwamret Yahaya Soje Ya Nemi A Saki Sowore

June 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.