Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Sanata Ahmed Mohammed Makarfi, ya musanta iƙirarin cewa za a iya yin maguɗin zaɓen babban zaɓen 2027, yana mai cewa irin waɗannan kalamai halayen ƴan siyasa ne da ba sa son yin aikin wahala da ake buƙata don cin zaɓe.
A cikin wata hira da ƴan jarida, Makarfi ya ce ya kamata ƴan siyasa su mayar da hankali wajen samun magoyon baya da ƙarfafa tsarin jam’iyyunsu, da kare sahihancin tsarin zaɓe maimakon yin zargin cewa ana shirin yin maguɗi tun da wuri.
Da yake mayar da martani kan damuwar da ake nunawa a wasu sassa cewa zaɓen gaba zai iya samun matsala, tsohon gwamnan ya ce ƴan siyasar da ke yin hasashen maguɗin zaɓe tun kafin a fara kaɗa ƙuri’a kawai suna neman uzuri ne.
“Kawai wannan tunanin mutum mai kasala ne, tun daga farko, zai ce za a yi maguɗin zaɓe a 2027.
“Me ya sa za ka tashi ka bar zaɓe? Ka yi aiki don ka ci zaɓe, ka yi aiki don ka hana maguɗi, amma me ya sa za ka riƙa cewa abubuwa ba za su yi daidai ba? A’a, abubuwa suna daidai, sai dai idan mu muka bari su zama ba daidai ba,” in ji Makarfi.
Makarfi ya yi wannan bayani ne a daidai lokacin da ake ƙara samun haɗakar siyasa gabanin zaɓen 2027, inda jam’iyyun adawa da masu ruwa da tsaki ke nuna damuwa kan yadda za a gudanar da zaɓen.
Tsohon shugaban kwamitin riƙo na jam’iyyar PDP ya bayyana cewa maimakon haifar da tsoro da rashin yarda a tsarin zaɓe, ya kamata jam’iyyun siyasa su mai da hankali kan tsayar da nagartattun ƴan takara da kuma shawo kan ƴan Nijeriya su mara musu baya.
Ya kuma jaddada cewa dimokiraɗiyya tana bunƙasa ne idan ƴan siyasa suna shiga zaɓe cikin tsari da gaskiya maimakon yin hasashe kan sakamakon tun kafin a fara yaƙin neman zaɓe.
Game da halin da PDP ke ciki, Makarfi ya nuna kwarin gwiwa cewa jam’iyyar na da karfin gaske duk da ƙalubalen da take fuskanta.
“Tabbas, daga cikin dukkan jam’iyyun siyasa, ina ganin PDP, saboda tana da tushe mai ƙarfi kuma ba ta dogara da mutum guda ba, tana da makoma mai kyau.”
Sai dai ya amince cewa jam’iyyar ta fuskanci matsaloli kuma mambobinta sun samu rarrabuwan wajen kaɗa ƙuri’a a zaɓen shugaban ƙasa na baya, abin da ya ce yana nuna gaskiyar siyasa ta lokacin.
A cewarsa, zaɓe yana shafar abubuwa da dama, ciki har da biyayya ga jam’iyya, ƙabila, addini, cancantar ɗan takara da kuma yanayin da ake ciki.
“Wasu mutane za su zaɓa ne saboda jam’iyya. Wasu saboda addini ko ƙabila. Wasu kuma kawai saboda ba sa son wani,” in ji shi.
Makarfi ya ce babu wani ɗan takara ko jam’iyya da ya kamata ya ɗauka cewa nasara ta tabbata tun kafin zaɓen 2027, yana mai gargaɗin cewa ƴan Nijeriya suna ƙara wayewa wajen zaɓar shugabanni.
“Waɗanda ke cikin takara suna da aiki mai yawa a gabansu. Duk wanda yake tunanin zai zauna kawai nasara ta riga ta tabbata, yana raina hankalin ƴan Nijeriya,” in ji shi.
Tsohon gwamnan ya kuma sake jaddada cewa dole ne jam’iyyun siyasa su bi dokokin zaɓe da ƙa’idoji yayin fafutukar siyasa, yana mai cewa mutunta doka na da matuƙar muhimmanci wajen ƙarfafa tsarin dimokiraɗiyyar Nijeriya.














