Bayan wasu makonni da jam’iyyun APC da PDP da ADC da NDC da kuma LP suka kammala zaɓen fid da gwani, har yanzu jam’iyyun ba su fitar da jerin sunayen ƴan takara na ƙarshe ba, wanda hakan ke jawo damuwa kan makomar siyasar ƴan takarar.
Rahotanni sun bayyana cewa duk da sanarwar da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), ta yi kwanan nan cewa za ta ba dukkan jam’iyyun siyasa lambobin sirri na hukuma don amfani da adireshinta a ranar Jumma’a, 26 ga Yuni, 2026, wajen saka sunayen, sai dai makomar ƴan takara a zaɓukan fitar da gwani na jam’iyyun a baya-bayan nan ba sa da tabbas.
Yayin da jam’iyyun siyasa suka kammala zaɓen fitar da gwani a makonni da suka wuce, sun ƙi fitar da jerin sunayen ƴan takarar gwamnan jihohi da na ƴan majalisar tarayya da kuma na majalisar jihohi na zaɓen 2027.
Rashin saka sunayen ya haifar da zarge-zargen siyasa mai yawa a cikin jam’iyyun.
An gano cewa jam’iyyun siyasa na ɓoye jerin sunayen ƴan takara ne da gangan don tabbatar da cewa lokacin da aka fitar da sunayen, zai zama tashin hankali ga ƴan takara da suka fusata don kai ƙara da ƙalubalantar tsarin da aka bi wajen zaɓen fitar da gwani.
A yayin da APC ta bayyana cewa jerin zai fito nan ba da jimawa ba, reshen PDP da ministan Babban Birnin Tarayya Abuja, Mista Nyesom Wike, yake jagoranta, shi ma ya shaida cewa suna jiran taron shugabannin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar don fitar da sunayen.
Sai dai da take kare matakinta na rashin fitar da sunayen ƴan takarar da suka yi nasara daga zaɓen fitar da gwani a fili, jam’iyyar NDC ta nace cewa babu wani doka da ke tilasta wa jam’iyyun siyasa yin hakan.
A nata ɓangaren, ADC ta ce har yanzu tana cikin bin jadawalin INEC da ƙa’idojin gabatar da sunayen ƴan takara. A gefe guda, LP ta ce ta amince da jerin sunayen kuma za ta fara loda su zuwa adireshin INEC a ranar 28 ga Yuni.
A cikin jam’iyyar APC, shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya nuna ƙaruwar samun fusata a tsakanin ƴan majalisa da suka faɗi zaɓen fitar da gwani.
Akpabio, yayin da yake magana a lokacin taron ƙaddamar da kwamitin yaƙin neman zaɓe na ƙasa na jam’iyyar APC don zaɓen gwamnan Ekiti, ya buƙaci shugabannin jam’iyyar su kula da jerin sunayen ƴan takara na ƙarshe da hankali.
Ya ce wasu daga cikin abokan aikinsa a majalisar ƙasa sun fusata sakamakon zaɓe fitar da gwani.
“Jam’iyya ce mafi girma. Ni dai ina roƙon jam’iyyar kawai ta tabbatar cewa idan sun saki jerin sunaye na ƙarshe, su haɗa da mu duka. Wasu daga mutanena suna ta ƙorafi,” in ji shi.
A ɓangarenta, NDC ta yi iƙirarin cewa babu wani doka da ke tilasta wa jam’iyyun siyasa su bayyana jerin sunayensu. Yayin da yake magana da manema labarai, sakataren jam’iyyar na ƙasa, Mista Osa Director, ya yi watsi da suka kan yadda jam’iyyar ke tafiyar da tsarin zaɓen ƴan takara, yana mai jayayya cewa dokar da ke kula da zaɓen cikin jam’iyya ba ta wajabta a bayyane a sake sunayen ƴan takara da suka samu nasara.
Ya tsaya kan cewa ƴan takara da suka fafata a zaɓen sun riga sun samu bayani game da sakamakon, yayin da waɗanda ba su gamsu da sakamakon ba suna da ƴancin zuwa kotu.
“Dokar ba ta buƙatar bayyana sakamakon ga jama’a ba,” in ji shi.
Ya bayyana cewa NDC ta bi dukkan dokokin da suka wajaba, yana mai cewa INEC tuni tana da bayanan da suka dace daga zaɓen fitar da gwanin.
Mai magana da yawun NDC ya ƙara fayyace cewa ranar 26 ga Yuni da aka kayyade na bayanan ƴan takara ga hukumar zaɓe an yi shi ne don bai wa jam’iyyun siyasa damar lodawa da tabbatar da jerin sunayensu na ƙarshe.
Haka kuma a martaninsa kan batun, PDP mai goyan bayan Wike ta ce tana jiran taron shugabannin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar don amincewa da jerin dukkan ƴan takara.
A cewar sakataran harkokin yaɗa labarai na PDP, Haruna Jungudo, “Mun gudanar da dukkan ayyukan zaɓe na neman ɗan takara, ciki har da ƙorafe-ƙorafen waɗanda suka ji ba su da gaskiya a yadda aka gudanar da aikin.”
“Aikinmu a wannan ɓangaren, duka aikin zaɓen fitar da gwani da ƙarar da aka shigar daga baya, INEC ta sanya ido a kai.
“Yanzu muna jiran taron shugabannin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar wanda ake sa ran zai gudana nan ba da jimawa ba don tabbatar da aikin. Sai dai bayan taron shugabannin kwamitin gudanarwa na jam’iyyar an tabbatar da shi ne kawai mu a matsayin jam’iyyar siyasa za mu ɗora sakamakon zaɓe a INEC”, in ji Jungudo.
Haka kuma, ADC ta ce ta kammala dukkan ayyukanta, amma ta jaddada cewa har yanzu tana cikin tsarin lokaci da ƙa’idojin INEC na miƙa sunayen ƴan takarar da aka zaɓa.
A yayin da yake magana da ƴan jarida, sakataren yaɗa labarai na ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya ce jam’iyya ta kammala dukkan ayyuka, ciki har da zaɓen ƴan takara na jam’iyyar da za su fafata a zaɓen 2027, amma tana jirar lokaci ne kawai.
Ita kuwa jam’iyyar LP ƙarƙashin jagorancin, Nenadi Usman ta ce ta amince da ƴan takarar 1,211 a hukumance domin yin takara a muƙamai daban-daban a zaɓen 2027.
Sakataren yaɗa labarai na ƙasa na jam’iyya, Ken Asogwa, ya ce kwamitin gudanarwa na jam’iyyar ya amince da dukkan ƴan takarar da aka zaɓa a zaɓen fitar da gwani, kuma jam’iyyar za ta fara ɗora sunayensu a shafin a INEC a ranar 28 ga Yuni.














