A ranar 20 ga watan Mayu, kasashen Sin da Rasha suka fitar da sanarwar hadin gwiwa mai goyon bayan rarrabuwar iko tsakanin kasashe daban daban maimakon wasu ‘yan tsiraru kalilan, da sabon salon dangantakar kasa da kasa, wadda ta yi bayani kan wasu shawarwari 4 na inganta samar da duniya mai adalci da tsari, inda kasashe daban daban ke da karfi, tare da gina sabon salon dangantakar kasa da kasa.
Wannan na zaman amsa ga tambayar da ake yi a zamanin yau cewa: “Ina dangantakar kasa da kasa ta nufa?” Bayanai daga jerin nazarce-nazarcen jin ra’ayoyin jama’a da kafar CGTN ta gudanar sun nuna cewa, ka’idojin mutunta juna da adalci da daidaito da hadin gwiwar moriyar juna, da sabon salon dangantakar kasa da kasa ke karfafawa, sun zama wani abu da kasa da kasa suka amince da shi.
A cewar wani nazarin CGTN kaso 84.1 na masu bayar da amsa sun yi imanin cewa, girmama mabanbantan hanyoyin neman ci gaba tsakanin kasashe, sharadi ne na hadin gwiwar kasa da kasa.
Haka kuma, wasu 85.6 na ganin cewa, tsaro shi ne sharadin neman ci gaba, kuma sun goyi bayan Shawarar Tsaron Duniya da Sin ta gabatar. Kimanin kaso 80.8 kuma, sun bayyana adawa da babakere da takunkumai daga bangare guda. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post