ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abun Da Za Ku So Sani Game Da Sabon Mai Rikon Shugaban ‘Yansanda Egbetokun

by Muhammad
3 years ago
Egbetokun

A daren ranar Litinin din nan ne shugaban kasa, Bola Tinubu, ya nada mataimakin babban sufeton ‘yan sandan Nijeriya DIG Kayode Egbetokun, a matsayin mukaddashin babban sufeton ‘yan sandan Nijeriya gabanin majalisar dattawat a tabbatar da shi.

Har zuwa nadin nasa na baya-bayan nan, Egbetokun an ba shi mukamin Mataimakin Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda kuma mai kula da shiyyar Kudu-maso-Yamma a matsayin mai kula da sashen binciken manyan laifuka (FCID) a hedkwatar rundunar ’Yansanda da ke Abuja tun ranar 6 ga Afrilu, 2023.

  • Da Dumi-Duminsa: Tinubu Ya Kori Hafsoshin Tsaron Nijeriya, Ya Nada Sabbi
  • Tinubu Ya Kori Shugabannin Hukumomi Da Ma’aikatu Da Cibiyoyin Gwamnati

An haifi sabon shugaban ’Yansandan ne a ranar 4 ga Satumba, 1964 a Erinja, karamar hukumar Yewa ta Kudu a Jihar Ogun kuma ya shiga aikin ‘Yansandan Nijeriya a ranar 3 ga Maris, 1990, a matsayin Mataimakin Sufeto na ‘Yansanda na sashen Cadet.

ADVERTISEMENT

Ya samu horo na farko a makarantar ‘Yansanda ta Nijeriya, kuma ya halarci kwasa-kwasai da dama a ciki da wajen rundunar ‘Yansanda.

Ya yi aiki a wasu rundunonin ‘Yansanda da a fadin kasar nan, kuma ya rike mukaman kwamanda a lokuta daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

A matsayinsa na Mataimakin Sufurtandan ‘Yansanda a shekarar 1999, an nada shi babban jami’in tsaro ga zababben gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu, wanda yanzu ya zama shugaban Nijeriya.

Ya yi aiki a matsayin Kwamanda, Rapid Response Squad (RRS), Lagos, Squadron Commander MOPOL da mukamin Anti-Fraud Unit, FCT, Abuja ya kuma zama Babban Sufeton ‘Yansandan gudanarwa na Hedkwatar Rundunar Jihar Legas, Ikeja da kuma Kwamandan shiyya a Osogbo na Rundunar ‘Yansandan jihar Osun kuma kwamandan yanki a Gusau, reshen jihar Zamfara da dai sauransu.

Egbetokun ba jami’in ‘Yansanda ne kadai ba, masanin lissafi ne. Ya kammala karatunsa na farko a Jami’ar Legas, Akoka, inda ya yi digirinsa na farko a fannin lissafi a watan Yuni 1987, sannan ya karantar da ilimin lissafi a Kwalejin Fasaha ta Yaba da ke Legas, kafin ya shiga aikin ‘Yansanda.

Sauran karatuttukansa sun hada da digiri na biyu a sashen nazarin fasaha a Jami’ar Legas, Akoka, 1996, PGD a fannin tattalin arzikin man fetur daga Jami’ar Jihar Delta, Abraka, 2000, da MBA daga Jami’ar Jihar Legas, Ojo a 2004.

Egbetokun
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Ba Da Gudummawar Kayayyakin Masu Amfani Da Mafi Karancin Makamashi Don Taimakawa Masar Wajen Yaki Da Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Ba Da Gudummawar Kayayyakin Masu Amfani Da Mafi Karancin Makamashi Don Taimakawa Masar Wajen Yaki Da Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.