ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abun Da Za Ku So Sani Game Da Sabon Mai Rikon Shugaban ‘Yansanda Egbetokun

by Muhammad
3 years ago
Egbetokun

A daren ranar Litinin din nan ne shugaban kasa, Bola Tinubu, ya nada mataimakin babban sufeton ‘yan sandan Nijeriya DIG Kayode Egbetokun, a matsayin mukaddashin babban sufeton ‘yan sandan Nijeriya gabanin majalisar dattawat a tabbatar da shi.

Har zuwa nadin nasa na baya-bayan nan, Egbetokun an ba shi mukamin Mataimakin Sufeto-Janar na ‘Yan Sanda kuma mai kula da shiyyar Kudu-maso-Yamma a matsayin mai kula da sashen binciken manyan laifuka (FCID) a hedkwatar rundunar ’Yansanda da ke Abuja tun ranar 6 ga Afrilu, 2023.

  • Da Dumi-Duminsa: Tinubu Ya Kori Hafsoshin Tsaron Nijeriya, Ya Nada Sabbi
  • Tinubu Ya Kori Shugabannin Hukumomi Da Ma’aikatu Da Cibiyoyin Gwamnati

An haifi sabon shugaban ’Yansandan ne a ranar 4 ga Satumba, 1964 a Erinja, karamar hukumar Yewa ta Kudu a Jihar Ogun kuma ya shiga aikin ‘Yansandan Nijeriya a ranar 3 ga Maris, 1990, a matsayin Mataimakin Sufeto na ‘Yansanda na sashen Cadet.

ADVERTISEMENT

Ya samu horo na farko a makarantar ‘Yansanda ta Nijeriya, kuma ya halarci kwasa-kwasai da dama a ciki da wajen rundunar ‘Yansanda.

Ya yi aiki a wasu rundunonin ‘Yansanda da a fadin kasar nan, kuma ya rike mukaman kwamanda a lokuta daban-daban.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

A matsayinsa na Mataimakin Sufurtandan ‘Yansanda a shekarar 1999, an nada shi babban jami’in tsaro ga zababben gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu, wanda yanzu ya zama shugaban Nijeriya.

Ya yi aiki a matsayin Kwamanda, Rapid Response Squad (RRS), Lagos, Squadron Commander MOPOL da mukamin Anti-Fraud Unit, FCT, Abuja ya kuma zama Babban Sufeton ‘Yansandan gudanarwa na Hedkwatar Rundunar Jihar Legas, Ikeja da kuma Kwamandan shiyya a Osogbo na Rundunar ‘Yansandan jihar Osun kuma kwamandan yanki a Gusau, reshen jihar Zamfara da dai sauransu.

Egbetokun ba jami’in ‘Yansanda ne kadai ba, masanin lissafi ne. Ya kammala karatunsa na farko a Jami’ar Legas, Akoka, inda ya yi digirinsa na farko a fannin lissafi a watan Yuni 1987, sannan ya karantar da ilimin lissafi a Kwalejin Fasaha ta Yaba da ke Legas, kafin ya shiga aikin ‘Yansanda.

Sauran karatuttukansa sun hada da digiri na biyu a sashen nazarin fasaha a Jami’ar Legas, Akoka, 1996, PGD a fannin tattalin arzikin man fetur daga Jami’ar Jihar Delta, Abraka, 2000, da MBA daga Jami’ar Jihar Legas, Ojo a 2004.

Egbetokun
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Ba Da Gudummawar Kayayyakin Masu Amfani Da Mafi Karancin Makamashi Don Taimakawa Masar Wajen Yaki Da Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Ba Da Gudummawar Kayayyakin Masu Amfani Da Mafi Karancin Makamashi Don Taimakawa Masar Wajen Yaki Da Sauyin Yanayi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.