Ɗan takarar kujerar Sanatan Zamfara ta Arewa a ƙarƙashin jam’iyyar APC, Dr. Sani Abdullahi Shinkafi, ya bayyana cewa wakilan yankin da suka yi sanata cikin shekaru 28 da suka gabata sun gabatar da ƙasa da kudirin dokoki 10 kacal.
Shinkafi ya bayyana hakan ne a Abuja jim kaɗan bayan ya miƙa fom ɗinsa na tsayawa takara, inda ya ce ya shiga takara ne domin ya gyara abin da ya kira ƙarancin wakilci da ya jefa yankin baya a fagen ci gaban ƙasa.
Ya ce daga shekarar 1999 zuwa yau, kujerar sanata ta Zamfara ta Arewa ta kasance tana karkata ne a hannun wasu yankuna, abin da ya sa wasu sassan yankin ke jin an ware su daga ci gaba da wakilci.
A cewarsa, yankin ya ƙunshi ƙananan hukumomi huɗu, amma ba a ba su cikakken wakilci na gaskiya ba a Majalisar Dattawa, yana mai cewa hakan ya haifar da rashin adalci da rashin daidaito a siyasa.
Shinkafi ya kuma koka cewa duk da yawan shekarun da wakilan yankin suka shafe a majalisa, ba su kawo manyan ayyukan gwamnatin tarayya masu tasiri a yankin ba, musamman a fannin ilimi da ci gaban tattalin arziki.
Ya bayyana cewa lokaci ya yi da za a kawo sauyi, yana mai cewa zai tsaya tsayin daka don ganin an samu sabon salo na wakilci a yankin Zamfara ta Arewa.
Dangane da batun tsarin zaɓen fidda gwani, Shinkafi ya ce bai yarda da tsarin sasanci ba, yana mai cewa zai tsaya ne kawai kan tsarin zaɓen fidda gwani kai tsaye kamar yadda doka ta tanada.
Ya ce dole ne a bai wa kowane ɗan takara dama ya fafata, yana mai cewa “duk wanda ya yi nasara shi ne zai wakilci jam’iyya.”
A wani ɓangare kuma, ɗan takarar Sanatan Ekiti ta Arewa, Senator Ayo Arise, ya bayyana cewa ya koma takara ne saboda kiran al’ummarsa, na burin ya ci gaba da aikin da ya fara a baya a Majalisar Dattawa.
Ya ce ya taimaka wajen samar da Jami’ar Tarayya ta Oye-Ekiti wadda ta taimaka wajen bunƙasa ilimi da ci gaban yankin, kuma yana son ƙara faɗaɗa irin wannan ci gaba idan aka sake zaɓensa.
Ya ƙara da cewa zai bar wa jama’a su yanke hukunci kan wanda ya fi cancanta ya wakilce su a Majalisar Dattawa a 2027.















Discussion about this post