Jam’iyyar NNPP ta sanar da yin afuwa ga mambobinta da aka kora ko aka dakatar, tare da ba su damar komawa cikin jam’iyyar ba tare da gindaya wani sharaɗi mai tsauri ba.
Rahotanni sun nuna cewa wanda ya kafa jam’iyyar, Boniface Aniebonam, ne ya bayyana hakan, yana mai cewa matakin na daga cikin ƙoƙarin haɗa kan jam’iyyar gabanin zaɓen 2027.
Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa za ta bai wa dukkan ‘yan majalisa da sauran shugabannin da ke riƙe da muƙamai a ƙarƙashinta tikitin tsayawa takara kai tsaye domin sake neman zaɓe a 2027, ba tare da shiga fafatawar zaɓen fidda gwani ba.
Haka kuma, NNPP ta nuna aniyarta na amfani da tsarin sasanci wajen zaɓen ‘yan takara a wasu muƙamai, domin rage sabani da ƙarfafa haɗin kai a cikin jam’iyyar.
Masu nazarin siyasa na ganin cewa wannan mataki na iya taimakawa NNPP wajen dawo da ƙarfinta da kuma jawo sabbin mambobi, musamman a wannan lokaci da ake fuskantar sauye-sauyen siyasa gabanin zaɓen 2027.















Discussion about this post