ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci A Ƙara Addu’o’in Zaman Lafiya Yayin Bikin Babbar Sallah

by Sulaiman
4 weeks ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga al’ummar jihar da ma ɗaukacin Nijeriya da su ƙara dagewa wajen yin addu’o’in zaman lafiya da tsaro a yayin bikin Babbar Sallah na shekarar 2026.

Gwamnan ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon taya murnar Babbar Sallah da ya aikewa al’ummar jihar a ranar Laraba, inda ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar wannan babban biki na addinin Musulunci.

Babbar Sallah, wadda Musulmi ke gudanarwa duk shekara a ranar 10 ga watan Zul-Hijja, biki ne da ke nuna sadaukarwa da biyayya ga Allah, kamar yadda Annabi Ibrahim (A.S.) ya nuna cikakkiyar biyayya da miƙa wuya ga umarnin Ubangiji.

ADVERTISEMENT

A cikin saƙonsa, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana godiyarsa ga Allah bisa nasarar jigilar maniyyata aikin Hajji kai tsaye daga Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau, abin da ya bayyana a matsayin tarihi ga jihar.

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Musulmi murnar Babbar Sallah ta shekarar 2026,” in ji gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ya ce ibadar layya da ake gudanarwa a lokacin Eid el-Adha tana nuna biyayya irin ta Annabi Ibrahim (A.S.), sannan kuma tana daga cikin muhimman ibadun aikin Hajji da maniyyata ke aiwatarwa.

Gwamnan ya yi kira musamman ga al’ummar Zamfara da maniyyatan Hajji da su ci gaba da yin addu’o’i domin samun dawwamammen zaman lafiya da ci gaba a jihar da Nijeriya baki ɗaya.

Ya ce gwamnatinsa ta samu gagarumar nasara a yaƙin da ake yi da ’yan bindiga, lamarin da ya sa al’ummomin da suka tsere daga gidajensu sakamakon hare-hare suka fara komawa yankunansu.

A cewarsa, a makon da ya gabata ne gwamnatin jihar ta samu nasarar mayar da dubban mutane da suka rasa matsugunansu zuwa ƙauyensu na Fegin Kanawa da ke Ƙaramar Hukumar Gusau bayan sun shafe sama da shekara guda suna gudun hijira.

Gwamna Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da dawo da dukkan mutanen da rikice-rikice suka raba da muhallansu cikin aminci.

Ya bayyana cewa irin waɗannan nasarori ba za su samu ba sai da haɗin kai da addu’o’in jama’a, don haka ya buƙaci al’umma su ƙara himma wajen addu’a musamman a irin wannan lokaci mai albarka.

“Ina yi wa kowa fatan gudanar da bikin Babbar Sallah cikin lumana da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Daga bisani, gwamnan ya halarci sallar Eid tare da dubban jama’a a filin Idi na tsakiya da ke Gusau.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
A Karo Na Biyu, Mbappe Ya Lashe Kyautar Gwarzon Ɗan Wasan Shekara Na Real Madrid

A Karo Na Biyu, Mbappe Ya Lashe Kyautar Gwarzon Ɗan Wasan Shekara Na Real Madrid

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.