ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci A Ƙara Addu’o’in Zaman Lafiya Yayin Bikin Babbar Sallah

by Sulaiman
1 week ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga al’ummar jihar da ma ɗaukacin Nijeriya da su ƙara dagewa wajen yin addu’o’in zaman lafiya da tsaro a yayin bikin Babbar Sallah na shekarar 2026.

Gwamnan ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon taya murnar Babbar Sallah da ya aikewa al’ummar jihar a ranar Laraba, inda ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar wannan babban biki na addinin Musulunci.

Babbar Sallah, wadda Musulmi ke gudanarwa duk shekara a ranar 10 ga watan Zul-Hijja, biki ne da ke nuna sadaukarwa da biyayya ga Allah, kamar yadda Annabi Ibrahim (A.S.) ya nuna cikakkiyar biyayya da miƙa wuya ga umarnin Ubangiji.

ADVERTISEMENT

A cikin saƙonsa, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana godiyarsa ga Allah bisa nasarar jigilar maniyyata aikin Hajji kai tsaye daga Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau, abin da ya bayyana a matsayin tarihi ga jihar.

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Musulmi murnar Babbar Sallah ta shekarar 2026,” in ji gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Ya ce ibadar layya da ake gudanarwa a lokacin Eid el-Adha tana nuna biyayya irin ta Annabi Ibrahim (A.S.), sannan kuma tana daga cikin muhimman ibadun aikin Hajji da maniyyata ke aiwatarwa.

Gwamnan ya yi kira musamman ga al’ummar Zamfara da maniyyatan Hajji da su ci gaba da yin addu’o’i domin samun dawwamammen zaman lafiya da ci gaba a jihar da Nijeriya baki ɗaya.

Ya ce gwamnatinsa ta samu gagarumar nasara a yaƙin da ake yi da ’yan bindiga, lamarin da ya sa al’ummomin da suka tsere daga gidajensu sakamakon hare-hare suka fara komawa yankunansu.

A cewarsa, a makon da ya gabata ne gwamnatin jihar ta samu nasarar mayar da dubban mutane da suka rasa matsugunansu zuwa ƙauyensu na Fegin Kanawa da ke Ƙaramar Hukumar Gusau bayan sun shafe sama da shekara guda suna gudun hijira.

Gwamna Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da dawo da dukkan mutanen da rikice-rikice suka raba da muhallansu cikin aminci.

Ya bayyana cewa irin waɗannan nasarori ba za su samu ba sai da haɗin kai da addu’o’in jama’a, don haka ya buƙaci al’umma su ƙara himma wajen addu’a musamman a irin wannan lokaci mai albarka.

“Ina yi wa kowa fatan gudanar da bikin Babbar Sallah cikin lumana da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Daga bisani, gwamnan ya halarci sallar Eid tare da dubban jama’a a filin Idi na tsakiya da ke Gusau.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
A Karo Na Biyu, Mbappe Ya Lashe Kyautar Gwarzon Ɗan Wasan Shekara Na Real Madrid

A Karo Na Biyu, Mbappe Ya Lashe Kyautar Gwarzon Ɗan Wasan Shekara Na Real Madrid

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.