ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci A Ƙara Addu’o’in Zaman Lafiya Yayin Bikin Babbar Sallah

by Sulaiman
4 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga al’ummar jihar da ma ɗaukacin Nijeriya da su ƙara dagewa wajen yin addu’o’in zaman lafiya da tsaro a yayin bikin Babbar Sallah na shekarar 2026.

Gwamnan ya bayyana hakan ne cikin wani saƙon taya murnar Babbar Sallah da ya aikewa al’ummar jihar a ranar Laraba, inda ya taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar wannan babban biki na addinin Musulunci.

Babbar Sallah, wadda Musulmi ke gudanarwa duk shekara a ranar 10 ga watan Zul-Hijja, biki ne da ke nuna sadaukarwa da biyayya ga Allah, kamar yadda Annabi Ibrahim (A.S.) ya nuna cikakkiyar biyayya da miƙa wuya ga umarnin Ubangiji.

ADVERTISEMENT

A cikin saƙonsa, Gwamna Dauda Lawal ya bayyana godiyarsa ga Allah bisa nasarar jigilar maniyyata aikin Hajji kai tsaye daga Filin Jirgin Sama na Ƙasa da Ƙasa da ke Gusau, abin da ya bayyana a matsayin tarihi ga jihar.

“Ina taya ɗaukacin al’ummar Musulmi murnar Babbar Sallah ta shekarar 2026,” in ji gwamnan.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Ya ce ibadar layya da ake gudanarwa a lokacin Eid el-Adha tana nuna biyayya irin ta Annabi Ibrahim (A.S.), sannan kuma tana daga cikin muhimman ibadun aikin Hajji da maniyyata ke aiwatarwa.

Gwamnan ya yi kira musamman ga al’ummar Zamfara da maniyyatan Hajji da su ci gaba da yin addu’o’i domin samun dawwamammen zaman lafiya da ci gaba a jihar da Nijeriya baki ɗaya.

Ya ce gwamnatinsa ta samu gagarumar nasara a yaƙin da ake yi da ’yan bindiga, lamarin da ya sa al’ummomin da suka tsere daga gidajensu sakamakon hare-hare suka fara komawa yankunansu.

A cewarsa, a makon da ya gabata ne gwamnatin jihar ta samu nasarar mayar da dubban mutane da suka rasa matsugunansu zuwa ƙauyensu na Fegin Kanawa da ke Ƙaramar Hukumar Gusau bayan sun shafe sama da shekara guda suna gudun hijira.

Gwamna Lawal ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na tabbatar da dawo da dukkan mutanen da rikice-rikice suka raba da muhallansu cikin aminci.

Ya bayyana cewa irin waɗannan nasarori ba za su samu ba sai da haɗin kai da addu’o’in jama’a, don haka ya buƙaci al’umma su ƙara himma wajen addu’a musamman a irin wannan lokaci mai albarka.

“Ina yi wa kowa fatan gudanar da bikin Babbar Sallah cikin lumana da kwanciyar hankali,” in ji shi.

Daga bisani, gwamnan ya halarci sallar Eid tare da dubban jama’a a filin Idi na tsakiya da ke Gusau.

Zamfara
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
  • Sulaiman
    Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya
  • Sulaiman
    Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta
  • Sulaiman
    Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

MASU ALAKA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
A Karo Na Biyu, Mbappe Ya Lashe Kyautar Gwarzon Ɗan Wasan Shekara Na Real Madrid

A Karo Na Biyu, Mbappe Ya Lashe Kyautar Gwarzon Ɗan Wasan Shekara Na Real Madrid

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026
Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

Za A Gudanar Da Taron Koli Na Shugabannin Harkokin Masana’antu Da Cinikayya Na APEC Na 2026 A Shenzhen

September 10, 2026
Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

Amurka Ta Bai Wa Nijeriya Sabbin Kayan Yaƙi Domin Yaƙi Da Ta’addanci

September 10, 2026
Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

Xi Ya Bukaci A Kara Azamar Dakile Aukuwar Muggan Hadurra Sakamakon Aukuwar Gobara A Wani Jirgin Ruwan Dakon Kayayyaki

September 10, 2026
Zamfara

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Zamfara

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.