Alƙalin Kotun Shari’a, Mohammed Muktar, ya tsallake rijiya da baya a ranar Laraba bayan wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne sun kai hari harabar kotun da ke ƙauyen Gwarjo, Ƙaramar Hukumar Matazu ta Jihar Katsina.
Jaridar Daily Trust ta bayyana cewa, harin ya faru ne da misalin tsakar rana, lokacin da maharan ɗauke da makamai suka mamaye harabar kotun, suka riƙa harbe-harbe ba ƙaƙƙautawa, tare da neman sanin inda alƙalin yake.
Mazauna yankin sun shaida wa Daily Trust cewa Mohammed Muktar ya hango maharan tun daga nesa, lamarin da ya ba shi damar tserewa ta wata taga jim kaɗan kafin su isa cikin kotun.
Wani mazaunin yankin ya ce, “‘Yan bindigar sun shiga cikin kotun suna harbe-harbe tare da tambayar inda alƙalin yake. Cikin sa’a, ya riga ya tsere ta taga, sannan wani direban babur ya taimaka masa ya bar yankin kafin maharan su iso.”
Wani ganau ya ce maharan sun fusata matuƙa bayan sun gano cewa alƙalin ya tsere, inda suka yi barazanar kashe shi idan ya sake dawowa domin zaman shari’a a ƙauyen.
Sabon harin ya ƙara jefa al’ummar Gwarjo cikin fargaba, kasancewar yankin ya sha fuskantar hare-haren ‘yan bindiga a lokuta da dama.













