Wani alkalin babbar kotun tarayya dake Kano, Mohammed Nasir Yunusa, ya rasu bayan ya faɗi a falonsa ranar Alhamis da yamma.
Rahotanni sun ce an garzaya da Alƙalin zuwa asibiti bayan ya yanke jiki, inda likitoci suka tabbatar da rasuwarsa. Majiyoyi daga kotun tarayya da ke Abuja sun tabbatar da faruwar lamarin, tare da bayyana cewa an yi jana’izarsa ranar Juma’a bisa koyarwar addinin Musulunci.
Daraktan yaɗa labarai ta babbar kotun tarayya, Catherine Oby Christopher, ta tabbatar da rasuwar, tana mai cewa alƙalin ya rasu ne a asibiti a Kano.
Marigayi Justice Mohammed Nasir Yunusa ya jagoranci shari’o’i masu muhimmanci da suka jawo hankalin jama’a, ciki har da ƙarar da ta biyo bayan zaɓen 2023 kan takarar ‘yan jam’iyyar Labour Party a faɗin ƙasar nan, ciki har da tsohon gwamnan jihar Abia, Alex Otti.
Abokan aikinsa da na kusa da shi sun bayyana marigayin a matsayin mutum mai ƙwazo da jajircewa wajen gudanar da adalci.















Discussion about this post