Shugaban kwaleji ilimi Jihar Kogi, Dakta. Paul Femi Fashagba, ya bayyana an bada Satifiket waɗanda aka ɗauki shekaru masu yawa ba tare da, ba waɗanda suka kammala karatun ba wanda abin ya zarce fiye da shekara goma daga 2016 zuwa 2025, ɗaukar matakin ne ya kawo ƙarshen dogon lokacin da aka ɗauka ba a ba waɗanda suka kammala Kwalejin ilimi ta Jigar Kogi satifiket ɗin su.
Dakta.Fashagba ya bayyana hakan ne lokacin da yake ganwa da manema labarai, a Lokoja babban birnin Jihar, inda ya ce waɗanda suka kammala makaranta daga 2016 zuwa 2020 za su amshi Satifiket ɗin su tsakanin 18 ga Mayu zuwa 1 ga watan Yuni, 2026,yayin da waɗanda suka kammala karatunsu daga shekarar 2021,zuwa 2025 za a basu Satifiket ɗin su daga 2 ga watan Yuni zuwa 15 ga Yuni, 2026.
Ya ce dogon lokacin da aka ɗauka na rahin bada Satifiket ɗin a ƙarƙashi mulkin gwamnatoci da yawa,hakan yasa ɗalibai waɗanda suka kammala makarantar shiga wani mawuyacin hali, musamman ma wajen samun aikin yi da kuma samun damar ci gaba da karatu,hakan ya haɗu da suka da maganganun da basu dace ba,daga jama’a da kuma kafofin sadrwa na zamani.
Kamar yadda Shugaban makarantar ya ce, an kira taron ƴan jaridar ne domin ayi bayani kan dalilan da suka sa shi ne domin a bayyana dalilan da suka san aka ɗauki lokaci mai tsawo ba tare da bada Satifiket ɗin ba ga wanɗanda suka kammala makarantar, lamarin da ya kai fiye da shekara goma.
Fashagba ya bayyana lokacin da ya fara aiki a matsayin Shugaban Kwalkejin ta ilimi, ya fara ne da niyyar maganin matsalolin da sukƙ sa har aka samu jinkirin da ya yi sanadiyar rashin bada Satifiket a lokacin da ya dace ayi hakan,da kuma yadda za a kawo masalahar maganin lamarin.
Ya ce daga cikin matakan da aka ɗauka sun haɗa da an tuntuɓi Hukumar kulawa da harkokin kwalejojin ilimi domin a tabbatar da an bi duk an bi matakan da suka kamata ɗauka, waɗanda dama kowa ya san sai an yi hakan.
Shugaban ya ƙara bayyana cewa binciken da aka sa aka yi ya nuna fiye da ɗalibai 4,000 da suka kammala makarantar har yanzu basu amshi Satifiket ɗin su ba fiye da shekaru goma.
Ya ƙara jaddada cewa an buga Satifiket ɗin, an tabbatar komai ya yi daidai an kuma sa hannu, daganan kuma sai maganar rabawa/ badawa.
Ya bayyana Shugabannin Kwalejin sun kafa kwamiti wanda zai lura da yadda za a raba Satifiket domin a tabbatar da an bi ƙa’idojin da suka kamata domin ayi gaskiya da bin duk ƙa’idojin.















Discussion about this post