Ƙaramin Ministan Tsaro, Bello Matawalle, ya ce Allah ne kaɗai zai iya kawo cikakken ƙarshen matsalar rashin tsaro a Nijeriya, duk da ƙoƙarin da gwamnati da jami’an tsaro ke yi wajen yaƙi da ‘yan ta’adda, da ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane.
Matawalle ya bayyana cewa matsalar tsaro ba ta Nijeriya kaɗai ba ce ke fama da ita, domin ƙasashe da dama a duniya na fuskantar irin wannan ƙalubale. Sai dai ya jaddada cewa gwamnati na ci gaba da ɗaukar matakai masu tsauri domin rage hare-hare da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
A cewarsa, nasarar yaƙi da rashin tsaro ba ta ta’allaka ga gwamnati kaɗai ba, yana mai kira ga al’umma su bai wa jami’an tsaro cikakken haɗin kai ta hanyar samar da sahihan bayanai kan lokaci domin gano masu aikata laifuka.
Kalaman ministan na zuwa ne yayin da hare-haren ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane ke ci gaba da tayar da hankali a sassan Arewa, lamarin da ke ƙara jawo kira ga gwamnati da ta ƙara ƙaimi wajen magance matsalar tsaro.















Discussion about this post