Rundunar ’Yansandan Birnin Landan ta Birtaniya (Metropolitan Police) ta tabbatar da kama wasu mutum uku da ake zargi da hannu a kisan wani mawaki dan asalin Nijeriya kuma dan kasar Birtaniya, Mark Orabiyi, wanda aka kashe ta hanyar caka masa wuka a lambun wani gida da ke kusa da titin Rayleigh Road.
Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, kamar yadda aka bayyana a cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin Intanet rundunar ’yansandan.
’Yansandan sun ce bayan samun rahoton faruwar lamarin, jami’an bincike sun garzaya wurin da abin ya faru inda suka tarar da Orabiyi da raunukan caka masa wuka. Duk da kokarin ma’aikatan agajin gaggawa, an tabbatar da mutuwarsa a wurin.
“Jami’an sun isa wurin tare da ma’aikatan Ambulance na Landan kuma suka tarar da wani mutum mai shekaru 35 da raunukan wuka a lambun wani gida da ke kusa da Rayleigh Road.
“Duk da kokarin ma’aikatan jinya, abin takaici an tabbatar da mutuwarsa a wurin.
“Ko da yake ba a kammala tantance gawar a hukumance ba, an bayyana sunan mamacin a matsayin Mark Orabiyi. Har yanzu jami’ai na musamman na ci gaba da bai wa iyalansa tallafi,” in ji sanarwar.
A cewar rundunar, iyalan mamacin sun bayyana shi a matsayin kaunataccen da, dan’uwa, kawu da kuma aboki.
“Mark kaunataccen da ne, dan’uwa, kawu da kuma aboki. Ya kawo soyayya, haske da farin ciki ga iyalinmu da kuma duk wanda ya san shi.
“Za mu ci gaba da tunawa da kyautatawarsa, kyakkyawar dabi’arsa da kuma baiwar da Allah ya yi masa. Kasancewarsa ta shafi rayuwar mutane da dama, kuma tarihinsa zai ci gaba da kasancewa a cikin zukatanmu har abada. Allah Ya jikansa da rahama,” kamar yadda iyalansa suka bayyana.
Sai dai rundunar ’yansandan ta ce an kama wasu mutane uku da ba a bayyana sunayensu ba dangane da lamarin.
Wadanda ake zargin sun hada da maza biyu da kuma mace guda.
Sanarwar ta kara da cewa: “An kama mutane uku a ranar Juma’a, 5 ga Yuni, bisa zargin kisan kai. Wani mutum mai shekaru 27 an sake shi bisa beli yayin da ake ci gaba da bincike.
“Bayan yi musu tambayoyi, an saki wani mutum mai shekaru 24 da kuma wata mace mai shekaru 25 ba tare da daukar wani karin mataki a kansu ba.”
Sanarwar ta kuma bayyana cewa wani mutum mai shekaru 20 ya samu raunukan caka masa wuka da dama a lamarin, amma ba su kai ga barazana ga rayuwarsa ba, kuma an kai shi asibiti domin jinya.
Da take mayar da martani, Babbar Jami’ar Bincike, Joanna Yorke, wadda ke jagorantar binciken, ta yi kira ga jama’a da su taimaka da bayanai domin gano gaskiyar abin da ya faru.
“Wannan lamari ne mai matukar tayar da hankali, kuma zuciyata tana tare da iyalan Mark da wadanda yake kauna.
“Bincikenmu na ci gaba cikin sauri. Ina kira ga duk wanda yake a yankin lokacin da lamarin ya faru da ya tuntubi ’yansanda.
“Muna son jin ta bakin duk wanda yake da bidiyon CCTB ko wani hoton bidiyo daga safiyar ranar da abin ya faru wanda zai taimaka mana a bincikenmu,” in ji Yorke.
A wani rahoto makamancin wannan, PUNCH Metro ta ruwaito cewa wata kotu a Birtaniya ta tsare wani mutum mai shekaru 32, Madwell Oguanaya, bisa zargin kashe wani dan Nijeriya mai shekaru 41, Taiwo Ekerin, bayan wani hari da ya faru a Lewisham da ke Landan.
Rundunar Met Police ta ce an tuhumi Oguanaya da laifin kisan kai bayan Ekerin ya mutu sakamakon raunukan da ya samu a wata arangama.














Discussion about this post