ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
3 weeks ago
Nijeriya

Rundunar ’Yansandan Birnin Landan ta Birtaniya (Metropolitan Police) ta tabbatar da kama wasu mutum uku da ake zargi da hannu a kisan wani mawaki dan asalin Nijeriya kuma dan kasar Birtaniya, Mark Orabiyi, wanda aka kashe ta hanyar caka masa wuka a lambun wani gida da ke kusa da titin Rayleigh Road.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, kamar yadda aka bayyana a cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin Intanet rundunar ’yansandan.

’Yansandan sun ce bayan samun rahoton faruwar lamarin, jami’an bincike sun garzaya wurin da abin ya faru inda suka tarar da Orabiyi da raunukan caka masa wuka. Duk da kokarin ma’aikatan agajin gaggawa, an tabbatar da mutuwarsa a wurin.

ADVERTISEMENT

“Jami’an sun isa wurin tare da ma’aikatan Ambulance na Landan kuma suka tarar da wani mutum mai shekaru 35 da raunukan wuka a lambun wani gida da ke kusa da Rayleigh Road.

“Duk da kokarin ma’aikatan jinya, abin takaici an tabbatar da mutuwarsa a wurin.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

“Ko da yake ba a kammala tantance gawar a hukumance ba, an bayyana sunan mamacin a matsayin Mark Orabiyi. Har yanzu jami’ai na musamman na ci gaba da bai wa iyalansa tallafi,” in ji sanarwar.

A cewar rundunar, iyalan mamacin sun bayyana shi a matsayin kaunataccen da, dan’uwa, kawu da kuma aboki.

“Mark kaunataccen da ne, dan’uwa, kawu da kuma aboki. Ya kawo soyayya, haske da farin ciki ga iyalinmu da kuma duk wanda ya san shi.

“Za mu ci gaba da tunawa da kyautatawarsa, kyakkyawar dabi’arsa da kuma baiwar da Allah ya yi masa. Kasancewarsa ta shafi rayuwar mutane da dama, kuma tarihinsa zai ci gaba da kasancewa a cikin zukatanmu har abada. Allah Ya jikansa da rahama,” kamar yadda iyalansa suka bayyana.

Sai dai rundunar ’yansandan ta ce an kama wasu mutane uku da ba a bayyana sunayensu ba dangane da lamarin.

Wadanda ake zargin sun hada da maza biyu da kuma mace guda.

Sanarwar ta kara da cewa: “An kama mutane uku a ranar Juma’a, 5 ga Yuni, bisa zargin kisan kai. Wani mutum mai shekaru 27 an sake shi bisa beli yayin da ake ci gaba da bincike.

“Bayan yi musu tambayoyi, an saki wani mutum mai shekaru 24 da kuma wata mace mai shekaru 25 ba tare da daukar wani karin mataki a kansu ba.”

Sanarwar ta kuma bayyana cewa wani mutum mai shekaru 20 ya samu raunukan caka masa wuka da dama a lamarin, amma ba su kai ga barazana ga rayuwarsa ba, kuma an kai shi asibiti domin jinya.

Da take mayar da martani, Babbar Jami’ar Bincike, Joanna Yorke, wadda ke jagorantar binciken, ta yi kira ga jama’a da su taimaka da bayanai domin gano gaskiyar abin da ya faru.

“Wannan lamari ne mai matukar tayar da hankali, kuma zuciyata tana tare da iyalan Mark da wadanda yake kauna.

“Bincikenmu na ci gaba cikin sauri. Ina kira ga duk wanda yake a yankin lokacin da lamarin ya faru da ya tuntubi ’yansanda.

“Muna son jin ta bakin duk wanda yake da bidiyon CCTB ko wani hoton bidiyo daga safiyar ranar da abin ya faru wanda zai taimaka mana a bincikenmu,” in ji Yorke.

A wani rahoto makamancin wannan, PUNCH Metro ta ruwaito cewa wata kotu a Birtaniya ta tsare wani mutum mai shekaru 32, Madwell Oguanaya, bisa zargin kashe wani dan Nijeriya mai shekaru 41, Taiwo Ekerin, bayan wani hari da ya faru a Lewisham da ke Landan.

Rundunar Met Police ta ce an tuhumi Oguanaya da laifin kisan kai bayan Ekerin ya mutu sakamakon raunukan da ya samu a wata arangama.

Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sace Ɗalibai: Gwamnatin Oyo Ta Sanya Dokar Hana Fita A Ƙananan Hukumomi 10

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

LABARAI MASU NASABA

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

Wakilin CMG Ya Zanta Da Mataimakin Shugaban Kasar Afirka Ta Kudu

July 4, 2026
CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

CAF Ta Gayyaci Ƙasashen Afirka Su Nemi Ɗaukar Nauyin Gasar AFCON Ta 2028, 2032 da 2036

July 4, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

Gwamnatin Zamfara Ta Jinjina Wa Shugaban NAHCON Kan Nasarar Aikin Hajjin 2026

July 4, 2026
Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

Tawaga Ta Biyu Ta Kwararrun Kasar Sin Ta Sauka A Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo Domin Karfafa Yaki Da Cutar Ebola

July 4, 2026
Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

Yadda Gidauniyar Ɗahiru Mangal Ta Tallafa Wa Marasa Lafiya 30,000 A Katsina

July 4, 2026
Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

Babban Dan Majalissar Dokokin Kasar Sin Ya Halarci Jana’izar Marigayi Jagoran Addini Na Iran

July 4, 2026
Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi

July 4, 2026
Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

July 4, 2026
Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

July 4, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC

July 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.