ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

by Rabi'u Ali Indabawa
5 hours ago
Nijeriya

Rundunar ’Yansandan Birnin Landan ta Birtaniya (Metropolitan Police) ta tabbatar da kama wasu mutum uku da ake zargi da hannu a kisan wani mawaki dan asalin Nijeriya kuma dan kasar Birtaniya, Mark Orabiyi, wanda aka kashe ta hanyar caka masa wuka a lambun wani gida da ke kusa da titin Rayleigh Road.

Jaridar PUNCH Metro ta ruwaito cewa lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, kamar yadda aka bayyana a cikin wata sanarwa da aka wallafa a shafin Intanet rundunar ’yansandan.

’Yansandan sun ce bayan samun rahoton faruwar lamarin, jami’an bincike sun garzaya wurin da abin ya faru inda suka tarar da Orabiyi da raunukan caka masa wuka. Duk da kokarin ma’aikatan agajin gaggawa, an tabbatar da mutuwarsa a wurin.

ADVERTISEMENT

“Jami’an sun isa wurin tare da ma’aikatan Ambulance na Landan kuma suka tarar da wani mutum mai shekaru 35 da raunukan wuka a lambun wani gida da ke kusa da Rayleigh Road.

“Duk da kokarin ma’aikatan jinya, abin takaici an tabbatar da mutuwarsa a wurin.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

“Ko da yake ba a kammala tantance gawar a hukumance ba, an bayyana sunan mamacin a matsayin Mark Orabiyi. Har yanzu jami’ai na musamman na ci gaba da bai wa iyalansa tallafi,” in ji sanarwar.

A cewar rundunar, iyalan mamacin sun bayyana shi a matsayin kaunataccen da, dan’uwa, kawu da kuma aboki.

“Mark kaunataccen da ne, dan’uwa, kawu da kuma aboki. Ya kawo soyayya, haske da farin ciki ga iyalinmu da kuma duk wanda ya san shi.

“Za mu ci gaba da tunawa da kyautatawarsa, kyakkyawar dabi’arsa da kuma baiwar da Allah ya yi masa. Kasancewarsa ta shafi rayuwar mutane da dama, kuma tarihinsa zai ci gaba da kasancewa a cikin zukatanmu har abada. Allah Ya jikansa da rahama,” kamar yadda iyalansa suka bayyana.

Sai dai rundunar ’yansandan ta ce an kama wasu mutane uku da ba a bayyana sunayensu ba dangane da lamarin.

Wadanda ake zargin sun hada da maza biyu da kuma mace guda.

Sanarwar ta kara da cewa: “An kama mutane uku a ranar Juma’a, 5 ga Yuni, bisa zargin kisan kai. Wani mutum mai shekaru 27 an sake shi bisa beli yayin da ake ci gaba da bincike.

“Bayan yi musu tambayoyi, an saki wani mutum mai shekaru 24 da kuma wata mace mai shekaru 25 ba tare da daukar wani karin mataki a kansu ba.”

Sanarwar ta kuma bayyana cewa wani mutum mai shekaru 20 ya samu raunukan caka masa wuka da dama a lamarin, amma ba su kai ga barazana ga rayuwarsa ba, kuma an kai shi asibiti domin jinya.

Da take mayar da martani, Babbar Jami’ar Bincike, Joanna Yorke, wadda ke jagorantar binciken, ta yi kira ga jama’a da su taimaka da bayanai domin gano gaskiyar abin da ya faru.

“Wannan lamari ne mai matukar tayar da hankali, kuma zuciyata tana tare da iyalan Mark da wadanda yake kauna.

“Bincikenmu na ci gaba cikin sauri. Ina kira ga duk wanda yake a yankin lokacin da lamarin ya faru da ya tuntubi ’yansanda.

“Muna son jin ta bakin duk wanda yake da bidiyon CCTB ko wani hoton bidiyo daga safiyar ranar da abin ya faru wanda zai taimaka mana a bincikenmu,” in ji Yorke.

A wani rahoto makamancin wannan, PUNCH Metro ta ruwaito cewa wata kotu a Birtaniya ta tsare wani mutum mai shekaru 32, Madwell Oguanaya, bisa zargin kashe wani dan Nijeriya mai shekaru 41, Taiwo Ekerin, bayan wani hari da ya faru a Lewisham da ke Landan.

Rundunar Met Police ta ce an tuhumi Oguanaya da laifin kisan kai bayan Ekerin ya mutu sakamakon raunukan da ya samu a wata arangama.

Nijeriya
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Da ‘Yan Sa-kai Sun Ceto Shanu 245 Da Aka Sace A Kaduna

June 6, 2026
Next Post
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.