Tun bayan kammala zaben fid da gwani na shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC, ɗan takarar shugaban ƙasar na jam’iyyar, Atiku Abubakar da sauran masu ruwa da tsaki sun matsa lamba ga tsohon gwamnan Jihar Ribas, Rotimi Amaechi, domin ya zama abokin takarar Atiku.
Atiku ya ziyarci Amaechi ba da jimawa ba bayan zaben fitar da gwani na neman ci gaba da goyon bayansa ga jam’iyya.
Jam’iyyar ADC ta zabi Amaechi a matsayin mataimakin ɗan takararta na shugaban ƙasa, domin tunkarar babban zaben 2027.
Rahotanni sun ce matakin na daga cikin dabarun jam’iyyar na ƙarfafa tikitinta a faɗin ƙasa. Amaechi, ya kasance tsohon gwamnan Jihar Rib kuma tsohon ministan sufuri, ya zo na biyu ne a zaben fid da gwani na jam’iyyar kafin daga bisani a zabe shi a matsayin mataimaki ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC.
ADC ta ce gogewarsa a mulki da siyasa za su taimaka wajen faɗaɗa karɓbuwar tikitin Atiku-Amaechi. Sai dai akwai ruɗani kan batun, domin wasu jami’an jam’iyyar sun ce ba a fitar da sanarwa a hukumance ba tukuna.
Mai magan da yawun jam’iyyar ADC, Bolaji Abdullahi, ya ce bai da tabbacin labarin a lokacin da aka tuntube shi, duk da cewa rahotanni da dama sun tabbatar da zabin.
Zabin Amaechi na zuwa ne yayin da ADC ke ƙoƙarin haɗa kan manyan ƴan adawa domin ƙalubalantar Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyarsa ta APC a zaben 2027.
Masu ruwa da tsaki na jam’iyya suna da ra’ayi mai kyau game da zabin Amaechi a matsayin abokin takarar Atiku.
Wata majiya ta shaida cewa rawar da Amaechi ya taka a baya a matsayin darakta janar na yaƙin neman zaben Buhari kafin ya bar APC na iya zama wata hanyar jan wasu mambobin jam’iyyu da suka fusata zuwa ADC.
Bayan taron ƴan adawa a Ibadan ta Jihar Oyo, an ce Atiku na tunanin zaben Gwamna Seyi Makinde a matsayin abokin takararsa.
Sai da kuma daga baya, Makinde ya yanke shawarar tsayawa takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar APM.














Discussion about this post