ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka_Isra’ila Akan Iran: Rikicin Gabas ta Tsakiya Ya Fara Daukar Sabon Salo

by Sulaiman
3 months ago
Iran

Tun bayan barkewar zanga-zangar tsadar rayuwa da ta rikide ta koma tarzomar kin jinin gwamnati daga wasu acikin al’ummar Iran a karshen Disamba 2025 da farkon Janairu 2026, an samu karuwar muhawara tsakanin Iran da Amurka, ciki har da tsauraran kalamai da barazanar juna tsakanin shugabannin kasashen biyu.

Amurka ta nuna goyon baya ga masu zanga-zangar ta Iran, tana kira ga gwamnatin Tehran da ta daina yin amfani da karfi wajen murkushe su, wanda hakan ya sanya Shugaba Donald Trump ya yi barazanar cewa, Washington na iya “taya” masu zanga-zangar ko ma daukar matakai idan hukumomin Iran suka yi amfani da karfi wajen kashe mutane.

  • ASUU Ta Ba Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana Hudu Kan Sabon Tsarin Albashi
  • UBEC Ta Kaddamar Da Tsarin Dala Miliyan 552 Domin Ilimin Bai-daya

A nata martanin, Iran ta zargi Amurka da tsoma baki sosai a harkokinta na cikin gida, tana cewa wannan wani yunkuri ne na kifar da gwamnatinta, wanda kuma ba za ta lamunci hakan ba. A cikin martanin da aka fitar a hukumance, Tehran ta yi gargadin cewa, duk wani yunkurin Washington na kai hari Tehran zai dagula zaman lafiyar yankin, inda ta sha alwashin mayar da martanin hari kan duk wani sansanin sojin Amurka dake yankin da kuma duk kasar da ta bari Amurka ta yi amfani da kasarta ko sararin samaniyarta wurin kai mata (Iran) hari.

ADVERTISEMENT

Amma Amurka ta yi biris da duk wannan martanin, inda a ranar 28 ga watan Fabrairu, ta hada kai da Isra’ila suka kaddamar da hare-hare cikin Iran wanda hakan ya yi sanadin mutuwar Babban jagoran addini na kasar, Ayatullah Alkamnei tare da wasu kwamandojin sojojin juyin juya hali (IRGC) na Iran.

Rahotanni na nuna cewa, bayan wata guda da fara hare-haren hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila kan Iran, yankin Gabas ta Tsakiya na kara fadawa cikin rikici mai tsanani, inda yawan mace-macen fararen hula ke karuwa, yayin da rikicin ke kara yaduwa zuwa wasu sassa na yankin.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

Bincike ya nuna cewa, wannan rikici bai zama dole ba, domin akwai hanyoyin diflomasiyya da za a iya bi kafin fara hare-haren amma aka yi watsi da su, sabida rashin girmama tsarin doka na Majalisar Dinkin Duniya, lamarin da ya kara dagula al’amura maimakon kawo mafita.

Masana harkokin kasa da kasa sun bayyana damuwa kan yadda aka kaddamar da wannan hare-haren na son rai, musamman dangane da rashin samun amincewar Majalisar Tsaro ta Majalisar Dinkin Duniya kafin daukar matakin soja, wanda hakan na iya kawo cikas ga dokokin kasa da kasa da kuma rage darajar tsarin doka a duniya.

Rahotanni sun nuna cewa, maimakon samun kwanciyar hankali da Amurka ta yi ikirarin samarwa, hare-harenta sun kara jefa yankin cikin wani hali mawuyaci. Tarihi ya nuna cewa, irin wadannan matakan hare-hare na Amurka, ba sa haifar da komai sai dai haddasa rashin zaman lafiya mai dorewa, kamar yadda aka gani a sauran kasashen da irin hakan ta faru da su, kamar Libya, Iraq, Afghanistan da Syria.

Masana sun jaddada cewa, hanyar soja kadai ba za ta iya kawo cikakken tsaro ba. Sun ce yankin na bukatar zaman lafiya, ci gaba da tattaunawa, da kuma hanyoyin siyasa domin warware matsalolin da ke akwai.

Sam bai dace ba, manyan kasashe su rika take kanana, kamar ana rayuwar dabbobin daji. Ya dace, kasashen duniya su guji daukar matakai na kashin kai, su kuma mutunta dokokin kasa da kasa domin tabbatar da adalci da zaman lafiya a duniya.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Iran
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Gyaran fuska

Yadda Fatar Ki Za Ta Yi Laushi Da Sheki

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.