ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amurka_Isra’ila Akan Iran: Rikicin Gabas ta Tsakiya Ya Fara Daukar Sabon Salo

by Sulaiman
5 months ago
Iran

Tun bayan barkewar zanga-zangar tsadar rayuwa da ta rikide ta koma tarzomar kin jinin gwamnati daga wasu acikin al’ummar Iran a karshen Disamba 2025 da farkon Janairu 2026, an samu karuwar muhawara tsakanin Iran da Amurka, ciki har da tsauraran kalamai da barazanar juna tsakanin shugabannin kasashen biyu.

Amurka ta nuna goyon baya ga masu zanga-zangar ta Iran, tana kira ga gwamnatin Tehran da ta daina yin amfani da karfi wajen murkushe su, wanda hakan ya sanya Shugaba Donald Trump ya yi barazanar cewa, Washington na iya “taya” masu zanga-zangar ko ma daukar matakai idan hukumomin Iran suka yi amfani da karfi wajen kashe mutane.

  • ASUU Ta Ba Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana Hudu Kan Sabon Tsarin Albashi
  • UBEC Ta Kaddamar Da Tsarin Dala Miliyan 552 Domin Ilimin Bai-daya

A nata martanin, Iran ta zargi Amurka da tsoma baki sosai a harkokinta na cikin gida, tana cewa wannan wani yunkuri ne na kifar da gwamnatinta, wanda kuma ba za ta lamunci hakan ba. A cikin martanin da aka fitar a hukumance, Tehran ta yi gargadin cewa, duk wani yunkurin Washington na kai hari Tehran zai dagula zaman lafiyar yankin, inda ta sha alwashin mayar da martanin hari kan duk wani sansanin sojin Amurka dake yankin da kuma duk kasar da ta bari Amurka ta yi amfani da kasarta ko sararin samaniyarta wurin kai mata (Iran) hari.

ADVERTISEMENT

Amma Amurka ta yi biris da duk wannan martanin, inda a ranar 28 ga watan Fabrairu, ta hada kai da Isra’ila suka kaddamar da hare-hare cikin Iran wanda hakan ya yi sanadin mutuwar Babban jagoran addini na kasar, Ayatullah Alkamnei tare da wasu kwamandojin sojojin juyin juya hali (IRGC) na Iran.

Rahotanni na nuna cewa, bayan wata guda da fara hare-haren hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila kan Iran, yankin Gabas ta Tsakiya na kara fadawa cikin rikici mai tsanani, inda yawan mace-macen fararen hula ke karuwa, yayin da rikicin ke kara yaduwa zuwa wasu sassa na yankin.

LABARAI MASU NASABA

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

Bincike ya nuna cewa, wannan rikici bai zama dole ba, domin akwai hanyoyin diflomasiyya da za a iya bi kafin fara hare-haren amma aka yi watsi da su, sabida rashin girmama tsarin doka na Majalisar Dinkin Duniya, lamarin da ya kara dagula al’amura maimakon kawo mafita.

Masana harkokin kasa da kasa sun bayyana damuwa kan yadda aka kaddamar da wannan hare-haren na son rai, musamman dangane da rashin samun amincewar Majalisar Tsaro ta Majalisar Dinkin Duniya kafin daukar matakin soja, wanda hakan na iya kawo cikas ga dokokin kasa da kasa da kuma rage darajar tsarin doka a duniya.

Rahotanni sun nuna cewa, maimakon samun kwanciyar hankali da Amurka ta yi ikirarin samarwa, hare-harenta sun kara jefa yankin cikin wani hali mawuyaci. Tarihi ya nuna cewa, irin wadannan matakan hare-hare na Amurka, ba sa haifar da komai sai dai haddasa rashin zaman lafiya mai dorewa, kamar yadda aka gani a sauran kasashen da irin hakan ta faru da su, kamar Libya, Iraq, Afghanistan da Syria.

Masana sun jaddada cewa, hanyar soja kadai ba za ta iya kawo cikakken tsaro ba. Sun ce yankin na bukatar zaman lafiya, ci gaba da tattaunawa, da kuma hanyoyin siyasa domin warware matsalolin da ke akwai.

Sam bai dace ba, manyan kasashe su rika take kanana, kamar ana rayuwar dabbobin daji. Ya dace, kasashen duniya su guji daukar matakai na kashin kai, su kuma mutunta dokokin kasa da kasa domin tabbatar da adalci da zaman lafiya a duniya.

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

 

Iran
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Umarnin Kawo Karshen Matsalar Tsaro
Rahotonni

Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja

September 5, 2026
Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
Rahotonni

Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed

September 5, 2026
Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
Rahotonni

Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki

September 5, 2026
Next Post
Gyaran fuska

Yadda Fatar Ki Za Ta Yi Laushi Da Sheki

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.