ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

by Muhammad Bashir
2 months ago

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sanya hannu kan Dokar Kasafin Kuɗi ta shekarar 2026, wadda ta tanadi jimillar kashe kuɗi na Naira tiriliyan 68.32.Haka kuma, ya amince da ƙudurin da ya tsawaita lokacin aiwatar da kasafin kuɗin 2025 daga ranar 31 ga Maris 2026, zuwa 30 ga Yunin 2026.

A cewar sanarwar mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, kasafin kuɗin na Naira tiriliyan 68.32 ya ware Naira tiriliyan 4.799 domin wasu ayyukan da suka jibanci al’amuran doka, sannan Naira tiriliyan 15.8 domin biyan bashin gwamnati.

  • Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
  • Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
  • Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
  • Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
  • 2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Haka kuma, an ware Naira tiriliyan 15.4 domin kuɗaɗen gudanarwa inda Naira tiriliyan 32.2 kuma aka keɓe wa Asusun Ci Gaba domin ayyukan ci gaba.Bugu da ƙari, Shugaban Ƙasar ya sanya hannu kan dokar gyaran kasafin kuɗi ta 2026, wadda ta tsawaita lokacin aiwatar da ɓangaren ayyukan ci gaba na kasafin 2025 daga 31 ga Maris 2026, zuwa 30 ga Yuni, 2026.

ADVERTISEMENT

Onanuga ya ce tsawaita aiwatar da kasafin zai tabbatar da cikakken amfani da kuɗaɗen da aka ware, musamman ga manyan ayyukan more rayuwa da ci gaba da suka kusa kammaluwa a faɗin ƙasarnanYa ƙara da cewa hakan zai bai wa Ma’aikatu da Hukumomi damar kammala ayyukan da suke yi da inganta yawan kammala ayyuka, tare da tabbatar da ingantaccen amfani da kuɗin jama’a.

Da zarar dokar kasafin kuɗin 2026 ta fara aiki daga ranar 1 ga Afrilu, Gwamnatin Tarayya za ta fara cikakken aiwatar da ita bisa tsarin shirin Renewed Hope.Shugaba Tinubu ya umarci ma’aikatu da hukumomi da su tabbatar da amfani da kuɗaɗe cikin tsari da gaskiya da inganci, tare da mai da hankali wajen kammala ayyuka a kan lokaci.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Ya kuma yaba wa shugabanci da ‘yan Majalisar Tarayya bisa jajircewa da haɗin kai da kishin ƙasa wajen duba da amincewa da kasafin cikin gaggawa.A ƙarshe, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya aniyarsa ta zurfafa gyare-gyaren tattalin arziki da ƙara hanyoyin samun kuɗaɗen shiga, da fifita zuba jari da za su bunƙasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da kuma ƙarfafa tsarin tallafin jin ƙai ga al’umma.

Muhammad Bashir
+ postsBio
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Inuwa Yahaya Ya Tsaya Takarar Sanatan Gombe Ta Arewa
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Gwamna Yusuf Ya Amince Da Fitar Da Biliyan 21.2 Don Gyaran Manyan Matatun Ruwa Na Kano
  • Muhammad Bashir
    https://hausa.leadership.ng/author/muhammad-bashir/
    Tinubu Zai Kammala Shekaru Takwas A Mulki Kamar Yadda Buhari Ya Yi – Onanuga

MASU ALAKA

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
Rahotonni

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
Labarai

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare
Labarai

Sace Dalibai 42:Shugabannin Uba Askira Sun Ce Hakurinsu Ya Kare

June 12, 2026
Next Post
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Na Naira Tiriliyan 68.32, Ya Tsawaita Ayyukan 2025

Ku Kula Da Kyawawan Ɗabi’u, Su Ne Waɗanda Annabi SAW Ya Kira Duk Halitta A Kansu

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026
Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya

June 13, 2026
Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

Africa CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwar Sin A Yakin Da Afrika Ke Yi Da Cutar Ebola

June 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.