Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sanya hannu kan Dokar Kasafin Kuɗi ta shekarar 2026, wadda ta tanadi jimillar kashe kuɗi na Naira tiriliyan 68.32.Haka kuma, ya amince da ƙudurin da ya tsawaita lokacin aiwatar da kasafin kuɗin 2025 daga ranar 31 ga Maris 2026, zuwa 30 ga Yunin 2026.
A cewar sanarwar mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, kasafin kuɗin na Naira tiriliyan 68.32 ya ware Naira tiriliyan 4.799 domin wasu ayyukan da suka jibanci al’amuran doka, sannan Naira tiriliyan 15.8 domin biyan bashin gwamnati.
- Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé
- Yadda Rufe Kan Iyakoki Ke Ci Gaba Da Zama Barazana Ga Tattalin Arzikin Nijeriya
- Mutum 53,000 Ke Mutuwa Duk Shekara Sakamakon Amfani Da Gurbataccen Abinci —Gwamnati
- Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
- 2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Haka kuma, an ware Naira tiriliyan 15.4 domin kuɗaɗen gudanarwa inda Naira tiriliyan 32.2 kuma aka keɓe wa Asusun Ci Gaba domin ayyukan ci gaba.Bugu da ƙari, Shugaban Ƙasar ya sanya hannu kan dokar gyaran kasafin kuɗi ta 2026, wadda ta tsawaita lokacin aiwatar da ɓangaren ayyukan ci gaba na kasafin 2025 daga 31 ga Maris 2026, zuwa 30 ga Yuni, 2026.
Onanuga ya ce tsawaita aiwatar da kasafin zai tabbatar da cikakken amfani da kuɗaɗen da aka ware, musamman ga manyan ayyukan more rayuwa da ci gaba da suka kusa kammaluwa a faɗin ƙasarnanYa ƙara da cewa hakan zai bai wa Ma’aikatu da Hukumomi damar kammala ayyukan da suke yi da inganta yawan kammala ayyuka, tare da tabbatar da ingantaccen amfani da kuɗin jama’a.
Da zarar dokar kasafin kuɗin 2026 ta fara aiki daga ranar 1 ga Afrilu, Gwamnatin Tarayya za ta fara cikakken aiwatar da ita bisa tsarin shirin Renewed Hope.Shugaba Tinubu ya umarci ma’aikatu da hukumomi da su tabbatar da amfani da kuɗaɗe cikin tsari da gaskiya da inganci, tare da mai da hankali wajen kammala ayyuka a kan lokaci.
Ya kuma yaba wa shugabanci da ‘yan Majalisar Tarayya bisa jajircewa da haɗin kai da kishin ƙasa wajen duba da amincewa da kasafin cikin gaggawa.A ƙarshe, ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya aniyarsa ta zurfafa gyare-gyaren tattalin arziki da ƙara hanyoyin samun kuɗaɗen shiga, da fifita zuba jari da za su bunƙasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da kuma ƙarfafa tsarin tallafin jin ƙai ga al’umma.















Discussion about this post