Jam’iyyar ADC na ci gaba da zawarcin tsohon ɗan takarar gwamnan Jihar Kano na APC, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna, inda take ƙoƙarin jawo hankalinsa da tayin tikitin takarar gwamna tare da ɗaukar nauyin yaƙin neman zaɓensa.
Daily Nigerian ta rawaito cewa, shugabannin jam’iyyar na ganin Gawuna a matsayin ɗaya daga cikin fitattun ‘yan siyasar da za su iya ƙara wa jam’iyya mai mulki ta APC a Jihar Kano gabanin babban zaɓen shekarar 2027.
Rahoton ya nuna tayin ya haɗa da ba shi tikitin takarar gwamna ba tare da wata gasa mai tsanani ba, tare da samar da tallafin kuɗaɗe domin gudanar da yaƙin neman zaɓe.
Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga Gawuna ko ADC da ta tabbatar da cikakken bayani kan wannan tayi.
Masu sa ido kan harkokin siyasa na ganin cewa duk wata yarjejeniya tsakanin ɓangarorin biyu za ta iya sauya yanayin siyasar Kano gabanin zaɓen 2027.














Discussion about this post