A jiya ranar 1 ga wata da dare, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya dawo birnin Beijing, bayan da ya kammala halartar kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC karo na 32 tare da gudanar da ziyarar aiki a kasar Koriya ta Kudu.
Idan ba mu manta ba, ziyararsa a kasar Koriya ta Kudu a wannan karo ta biyo bayan ziyarar da ya yi a kasar a shekaru 11 da suka wuce, kuma a wannan ziyarar, shugabannin kasashen biyu sun gana da juna, ganawar da ta kasance ta farko a tsakaninsu bayan da shugaba Lee Jae-myung ya hau kujerar shugabancin kasar. Wata babbar nasarar da aka cimma a wannan ziyara kuma ita ce, an sake tabbatar da huldar kasashen biyu a matsayin huldar abota ta hadin gwiwa bisa manyan tsare tsare.
Nasarar makwabta nasara ce ga wanda ke makwabtaka da ita. Yanzu haka huldar da ke tsakanin Sin da Koriya ta Kudu ta kyautata, wanda abu ne da ya kamata a darajanta. Kasancewar kasashen biyu makwabtan juna da ba za a iya raba su ba, kamata ya yi su tabbatar da daidaiton da shugabanninsu suka cimma, kuma su dada yin mu’amala da juna da kuma kusantar juna, sabo da hakan ba kawai zai haifar da alfanu ga al’ummominsu ba ne, har ma zai samar da kwarin gwiwa ga yankin Asiya da tekun Pasifik da ma duniya baki daya. (Lubabatu Lei)














