ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

by Rabi'u Ali Indabawa
7 months ago
Salam

Makabartar Wadi al-Salam da ke birnin Najaf a kasar Iraki, ita ce makabartar Musulmai da ta fi kowace makabarta girma a duniya.

An binne sama da mutum miliyan shida a cikinta, inda wasu kaburburan da ke ciki suka samo asali tun karnuka da suka gabata.

  • ‘Yansanda Sun Tabbatar Da Mutuwar Wata Ba’amurkiya Da Ta Ziyarci Saurayinta A Jihar Delta
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

Mafi yawan wadanda ake binnewa da kuma masu ziyara a makabartar mabiya akidar Shi’a ne.

ADVERTISEMENT

Makabartar na da girman da ya kai eka 1,485.5, kuma wuri ne da ke karbar bakuncin miliyoyin Musulmai masu ziyara a kowace shekara.

Ana ganin cewa kusancin makabartar da hubbaren Ali ibn Abi Talib, sahabin Annabi Muhammad na daga cikin abubuwan da suka kara daukaka darajar makabartar.

LABARAI MASU NASABA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Imam Ali shi ne halifan Annabi Muhammad na hudu a mahangar Ahlussunnan, amma mabiya mazhabar Shi’a na daukar sa a matsayin na farko daga cikin imamansu 12.

Wannan ya sanya akasarin mabiya Shi’a na Iraki kan bukaci a binne su a makabartar, kuma sanadiyyar saukin sufuri a zamunnan baya-bayan nan, wasu mabiya Shi’a daga kasashen duniya kan so a binne su a makabartar.

Tsarin makabartar ya kasance cakuduwa ce ta gine-ginen hubbarai irin na zamanin baya, da hanyoyi masu tsuku da suka ratsa ta cikinta da kuma wasu wurare da ake yi wa kallon masu tsarki.

 

Me ya sa ake kiran makabartar Wadi al-Salam?

Ana kiran makabartar da sunan Wadi al-Salam, wato ‘kwarin aminci’ ne saboda dalilai na tarihi da dama.

Dalilai na addini: Ana yi wa makabartar daukar mai daraja, tare da imanin cewa wadanda ke kwance a cikinta na cikin rahama.

Alaka da Imam Ali: Makabartar tana makwaftaka da kabarin Imam Ali bin Abi Talib a birnin Najaf, wanda hakan ya sa Musulmai, musamman mabiya akidar Shi’a ke girmama ta kuma suke kwadayin ganin an binne su a cikinta.

Girma: Makabartar ta kasance mafi girma a duniya, inda ta mamaye wuri mai girman gaske, kunshe da miliyoyin kaburbura, inda ta zamo tamakar wani birni na mamata.

Ziyara: Masu ziyara zuwa birnin Najaf, mai tsarki ga mabiya akidar Shi’a sukan bi ta cikin makabartar tare da karanta Fatiha da kuma yin addu’o’in samun rahama ga wadanda ke kwance, lamarin da ya mayar da wurin tamkar wuri na ziyarar ibada.

Wadannan dalilai ne suka sanya tuntuni aka yi wa wurin lakabi da ‘kwarin aminci’ tun asali, kuma ake ci gaba da kiranta da hakan har yanzu.

 

Tarihin kafuwar makabartar Wadi al-Salam

Makabartar ta samo asali ne tun kafin zuwan addinin Musulunci a lokacin Annabi Muhammad, inda tun kafin wancan lokaci ake binne mutane a wurin.

Wuri ne mai muhimmanci wanda ke karbar bakuncin masu bincike na kimiyya da masana addini, musamman mabiya Shi’a daga sassa daban-daban na duniya.

Wadi al-Salam na da kofofi da dama da ake bi wajen shigar ta, inda hakan ke saukake zirga-zirga ga masu ziyara, kuma yawancin wadannan kofofi na karuwa ne bisa fadadar makabartar.

A shekara ta 2016 ne Hukumar kula da ilimi da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana makabartar a matsayin daya daga cikin wuraren tarihi na duniya.

 

Kalubalen da makabartar ke fuskanta

Daya daga cikin manyan kalubalen da makabartar ke fuskanta shi ne karuwar mutane da ake binnewa a lokacin yaki.

Misali, a lokacin da aka yi fama da rikicin kungiyar ISIS a Iraki, yawan mutanen da ake binnewa a kowace rana a makabartar ya daga zuwa 150 ko 200 a kowace rana, daga gawa 80 zuwa 120 da aka saba.

Wannan ya sanya wuraren binne sabbin mamata ya yi karanci.

 

Farashin binne mamaci

Farashin binne mamaci a makabartar Wadi al-Salam ya danganta ne da lokaci da kuma halin da ake ciki na zaman lafiya.

Ya zuwa farkon shekara ta 2025, kudin sayen filin binne mamaci mai girman murabba’in mita 25 ya kai miliyan biyar na kudn kasar Iraki, wato kimanin Dala 4,100, inda hakan ya nunka farashin da ake biya a lokutan da ake zaman lumana sosai.

Salam
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

MASU ALAKA

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar
Manyan Labarai

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle
Manyan Labarai

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Next Post
Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al'ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.