Yau Juma’a, aka bude taron ministocin kula da harkokin cinikayya na kungiyar hadin gwiwar tattalin arziki ta kasashen Asiya da Pasifik (APEC), a birnin Suzhou na lardin Jiangsu dake gabashin kasar Sin .
Taken taron na yini 2, wanda ya zo karkashin jagorancin kasar Sin da ke shugabantar kungiyar a bana shi ne, “Gina Al’ummar Asia da Pasifik Domin Samun Wadata Tare.” Inda yayin taron za a tattauna kan muhimman batutuwa ciki har da dunkulewar tattalin arzikin yankin da mara baya ga hukumar kula da cinikayya ta duniya da hadin gwiwa a bangaren dijital da kuma tattalin arziki mai kare muhalli.
A cewar ministan kula da cinikayya na Sin Wang Wentao, a matsayinsa na muhimmin taro da ake gudanarwa a tsakiyar shekara, an dorawa taron ministocin nauyin bayar da gudunmuwar sakamako ga taron shugabannin APEC, haka kuma yana zaman ma’aunin yanayin manufofin tattalin arziki da cinikayya a yankin Asiya da Pasifik da sauran sassan duniya. (Fa’iza Mustapha)















Discussion about this post