ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Yan Sudan Da Chadi 20 A Kano Bisa Shigo Wa Nijeria Ba Bisa Ka’ida Ba

by Abubakar Sulaiman
5 months ago
Kano

Jami’an NSCDC reshen Jihar Kano sun cafke wasu mutane 20 daga ƙasashen waje a yankin Danbare na Karamar Hukumar Kumbotso kan shigo wa Nijeriya ba bisa ka’ida ba.

Kwamandan reshen jihar, Mohammed Hassan-Agalama, ya bayyana haka ranar Talata a lokacin ganawa da manema labarai a Kano, inda ya ce waɗanda ake zargin sun fito ne daga Sudan, da Chadi, da Kamaru, da Nijar. “Daga cikin wadanda ake zargin, ɗaya daga Kamaru, ɗaya daga Nijar, 12 daga Sudan, da shida daga Chadi,” in ji Hassan-Agalama.

  • Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa
  • Kano Pillars Ta Lallasa Bendel Insurance A Kano

Ya bayyana cewa cafke su ya biyo bayan samun sahihan bayanan da kuma aikin haɗin gwiwa na jami’an NSCDC. Bincike na farko ya nuna cewa mafi yawansu ba su da sahihan takardun tafiya ko shaida ta ainihi, abin da ya haifar da damuwa game da ayyukansu a cikin jihar. An kama wayoyi Android guda 10 daga hannunsu.

ADVERTISEMENT

Hassan-Agalama ya kara da cewa, “Jami’an Corps suna ci gaba da bincike da tantance waɗanda ake zargin domin gano manufarsu da yiwuwar alaƙarsu da duk wasu ayyuka na laifi. Kuma an sanar da hukumomin da suka dace, kuma ana daukar matakai bisa doka.” Ya kuma jaddada jajircewar NSCDC wajen kare kadarorin ƙasa da tabbatar da tsaro a cikin gida, yana kira ga jama’a da su kasance masu lura da bayar da bayanai cikin lokaci.

Daya daga cikin wadanda aka kama, Idrisa Ila daga Jamhuriyar Nijar, ya shaida wa manema labarai cewa yana zaune a Kano tsawon shekaru uku yana gudanar da harkokin kasuwanci. Ya ce ya haɗu da wasu daga cikin wadanda aka kama ta Facebook, inda suka shirya tafiya zuwa Sudan ta Chadi, suna amfani da Nijeriya ne a matsayin wurin wucewa. “Sun ce ba su da isasshen kuɗi don ci gaba da tafiyarsu zuwa Sudan, shi ne suka yanke shawarar zama a Nijeriya na ɗan lokaci,” in ji Ila. Ya kara da cewa, da farko sun fara neman wuri zaman na ɗan lokaci, inda suka aiko masa da kuɗi don ya samo musu gida, amma daga baya adadin mutane ya karu fiye da yadda aka zata.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

Jama’ar a yankin sun fara yin shakku saboda yawan mazauna gidan da kuma rashin iya magana da Hausa ko Turanci, abin da ya sa suka sanar da hukumomi. Ila ya tabbatar da cewa yana da takardu sahihai, amma ba zai iya tabbatar da matsayin doka na sauran ba, wadanda suka zauna a Kano fiye da kwana 10 kafin a cafke su.

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Iyalin El-Rufai Sun Bai Ministan Tsaro Wa’adin Kwana 7 Kan Zargin Rikicin Kudancin Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Atiku Ya Zargi Gwamnatin Tarayya Da Cin Bashi Kamar Mashayin Da Kuɗi Ya Ƙarewa
  • Abubakar Sulaiman
    Boko Haram Ta Kai Hari Adamawa, Ana Fargabar Mutuwar Mutane 11
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Sokoto, Sun Kashe Mutane 7, Sun Yi Garkuwa Da 12

MASU ALAKA

'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina
Labarai

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare
Labarai

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Next Post
Kano

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 4, Dukiyar Naira Biliyan 1 A Watan Maris

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.