ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Yan Sudan Da Chadi 20 A Kano Bisa Shigo Wa Nijeria Ba Bisa Ka’ida Ba

by Abubakar Sulaiman
4 months ago
Kano

Jami’an NSCDC reshen Jihar Kano sun cafke wasu mutane 20 daga ƙasashen waje a yankin Danbare na Karamar Hukumar Kumbotso kan shigo wa Nijeriya ba bisa ka’ida ba.

Kwamandan reshen jihar, Mohammed Hassan-Agalama, ya bayyana haka ranar Talata a lokacin ganawa da manema labarai a Kano, inda ya ce waɗanda ake zargin sun fito ne daga Sudan, da Chadi, da Kamaru, da Nijar. “Daga cikin wadanda ake zargin, ɗaya daga Kamaru, ɗaya daga Nijar, 12 daga Sudan, da shida daga Chadi,” in ji Hassan-Agalama.

  • Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa
  • Kano Pillars Ta Lallasa Bendel Insurance A Kano

Ya bayyana cewa cafke su ya biyo bayan samun sahihan bayanan da kuma aikin haɗin gwiwa na jami’an NSCDC. Bincike na farko ya nuna cewa mafi yawansu ba su da sahihan takardun tafiya ko shaida ta ainihi, abin da ya haifar da damuwa game da ayyukansu a cikin jihar. An kama wayoyi Android guda 10 daga hannunsu.

ADVERTISEMENT

Hassan-Agalama ya kara da cewa, “Jami’an Corps suna ci gaba da bincike da tantance waɗanda ake zargin domin gano manufarsu da yiwuwar alaƙarsu da duk wasu ayyuka na laifi. Kuma an sanar da hukumomin da suka dace, kuma ana daukar matakai bisa doka.” Ya kuma jaddada jajircewar NSCDC wajen kare kadarorin ƙasa da tabbatar da tsaro a cikin gida, yana kira ga jama’a da su kasance masu lura da bayar da bayanai cikin lokaci.

Daya daga cikin wadanda aka kama, Idrisa Ila daga Jamhuriyar Nijar, ya shaida wa manema labarai cewa yana zaune a Kano tsawon shekaru uku yana gudanar da harkokin kasuwanci. Ya ce ya haɗu da wasu daga cikin wadanda aka kama ta Facebook, inda suka shirya tafiya zuwa Sudan ta Chadi, suna amfani da Nijeriya ne a matsayin wurin wucewa. “Sun ce ba su da isasshen kuɗi don ci gaba da tafiyarsu zuwa Sudan, shi ne suka yanke shawarar zama a Nijeriya na ɗan lokaci,” in ji Ila. Ya kara da cewa, da farko sun fara neman wuri zaman na ɗan lokaci, inda suka aiko masa da kuɗi don ya samo musu gida, amma daga baya adadin mutane ya karu fiye da yadda aka zata.

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

Jama’ar a yankin sun fara yin shakku saboda yawan mazauna gidan da kuma rashin iya magana da Hausa ko Turanci, abin da ya sa suka sanar da hukumomi. Ila ya tabbatar da cewa yana da takardu sahihai, amma ba zai iya tabbatar da matsayin doka na sauran ba, wadanda suka zauna a Kano fiye da kwana 10 kafin a cafke su.

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa
  • Abubakar Sulaiman
    Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata
  • Abubakar Sulaiman
    Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

MASU ALAKA

Auto Draft
Labarai

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Kano
Manyan Labarai

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Kano
Labarai

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Next Post
Kano

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 4, Dukiyar Naira Biliyan 1 A Watan Maris

LABARAI MASU NASABA

Auto Draft

ADC Ta Buƙaci Tinubu Ya Bai Wa Waɗanda Aka Sace A Kaiama Da Borno Kulawa

July 27, 2026
Kano

Sojojin Ruwa Sun Cafke Jirgin Ruwa Maƙare Da Ɗanyen Mai Na Sata

July 26, 2026
Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

Sin Za Ta Ci Gaba Da Kare Ikon Mulkin Yankuna Da Hakkoki Da Moriyarta Ta Teku

July 26, 2026
Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

Xi Jinping Ya Mika Sakon Murnar Cika Shekaru 61 Da Samun ‘Yancin Kai Ga Shugaban Maldives

July 26, 2026
Kano

Shugaban Ƙasa Tinubu Ya Naɗa Sabon Mai Ba Shi Shawara

July 26, 2026
Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

Sin Ta Ayyana Shirin Ko-ta-kwana Na Samar Da Tallafin Gaggawa Ga Lardin Guangdong

July 26, 2026
Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

Fina-finan Kasar Sin Suna Haskakawa Tare Da Samar Da Dimbin Kudaden Shiga A Zangon Nuna Fina-finai Na Lokacin Zafi Na Bana

July 26, 2026
Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

Shugaban Senegal Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Taimakon Gina Zaurukan Gudanar Da Wasannin Gasar Olympics Ta Matasa

July 26, 2026
Kano

Ƴan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Alƙalin Babbar Kotu A Kebbi

July 26, 2026
Bala Mohammed

Sadakin Budurwa ₦3,000 Na Bazawara ₦1,500: Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaryata Batun

July 26, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.