ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 6, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Yan Sudan Da Chadi 20 A Kano Bisa Shigo Wa Nijeria Ba Bisa Ka’ida Ba

by Abubakar Sulaiman
3 months ago
Kano

Jami’an NSCDC reshen Jihar Kano sun cafke wasu mutane 20 daga ƙasashen waje a yankin Danbare na Karamar Hukumar Kumbotso kan shigo wa Nijeriya ba bisa ka’ida ba.

Kwamandan reshen jihar, Mohammed Hassan-Agalama, ya bayyana haka ranar Talata a lokacin ganawa da manema labarai a Kano, inda ya ce waɗanda ake zargin sun fito ne daga Sudan, da Chadi, da Kamaru, da Nijar. “Daga cikin wadanda ake zargin, ɗaya daga Kamaru, ɗaya daga Nijar, 12 daga Sudan, da shida daga Chadi,” in ji Hassan-Agalama.

  • Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa
  • Kano Pillars Ta Lallasa Bendel Insurance A Kano

Ya bayyana cewa cafke su ya biyo bayan samun sahihan bayanan da kuma aikin haɗin gwiwa na jami’an NSCDC. Bincike na farko ya nuna cewa mafi yawansu ba su da sahihan takardun tafiya ko shaida ta ainihi, abin da ya haifar da damuwa game da ayyukansu a cikin jihar. An kama wayoyi Android guda 10 daga hannunsu.

ADVERTISEMENT

Hassan-Agalama ya kara da cewa, “Jami’an Corps suna ci gaba da bincike da tantance waɗanda ake zargin domin gano manufarsu da yiwuwar alaƙarsu da duk wasu ayyuka na laifi. Kuma an sanar da hukumomin da suka dace, kuma ana daukar matakai bisa doka.” Ya kuma jaddada jajircewar NSCDC wajen kare kadarorin ƙasa da tabbatar da tsaro a cikin gida, yana kira ga jama’a da su kasance masu lura da bayar da bayanai cikin lokaci.

Daya daga cikin wadanda aka kama, Idrisa Ila daga Jamhuriyar Nijar, ya shaida wa manema labarai cewa yana zaune a Kano tsawon shekaru uku yana gudanar da harkokin kasuwanci. Ya ce ya haɗu da wasu daga cikin wadanda aka kama ta Facebook, inda suka shirya tafiya zuwa Sudan ta Chadi, suna amfani da Nijeriya ne a matsayin wurin wucewa. “Sun ce ba su da isasshen kuɗi don ci gaba da tafiyarsu zuwa Sudan, shi ne suka yanke shawarar zama a Nijeriya na ɗan lokaci,” in ji Ila. Ya kara da cewa, da farko sun fara neman wuri zaman na ɗan lokaci, inda suka aiko masa da kuɗi don ya samo musu gida, amma daga baya adadin mutane ya karu fiye da yadda aka zata.

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Jama’ar a yankin sun fara yin shakku saboda yawan mazauna gidan da kuma rashin iya magana da Hausa ko Turanci, abin da ya sa suka sanar da hukumomi. Ila ya tabbatar da cewa yana da takardu sahihai, amma ba zai iya tabbatar da matsayin doka na sauran ba, wadanda suka zauna a Kano fiye da kwana 10 kafin a cafke su.

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
  • Abubakar Sulaiman
    Enekweci Ne Zai Jagoranci Tawagar Nijeriya A Wasannin Commonwealth Na Bana
  • Abubakar Sulaiman
    Akwai Barazanar Ƙaruwar Yunwa A Arewacin Nijeriya – Peter Obi
  • Abubakar Sulaiman
    Kwankwasiyya Ta Buƙaci A Binciki Zargin Kasafin Kuɗin PFIPC

MASU ALAKA

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje
Labarai

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam
Labarai

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Next Post
Kano

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 4, Dukiyar Naira Biliyan 1 A Watan Maris

LABARAI MASU NASABA

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

FIFA Ta Dakatar Da Aiwatar Da Hukuncin Hana Folarin Balogun Buga Wasa

July 5, 2026
Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

Sabbin Shaidu Sun Bulla Dake Kara Tabbatar Da Ta’asar Amfani Da Sinadarai Masu Guba Yayin Da Dakarun Japan Ke Mamaya A Sassan Kasar Sin

July 5, 2026
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Tarayya Ta Nemi Taimakon Ƙasashen Waje

Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

July 5, 2026
An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

An Gabatar Da Littafin “Bayanan Xi Jinping Kan Basirar Gudanar Da Ayyuka A Kananan Hukumomi”

July 5, 2026
Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

Ko Kafa Ƴansandan Jihohi Zai Taimaka Wajen Kawo Ƙarshen Matsalolin Tsaro?

July 5, 2026
Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

Rashin Tarbiyya Da Ilimin Addini Ne Ke Sa Matasa Ɗaukar Doka a Hannu – Hon. Aminu Adam

July 5, 2026
Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

Kayayyakin Sin Sun Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

July 5, 2026
Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

Sin Da Rasha Za Su Gudanar Da Atisayen Sojojin Ruwa Da Sintiri Na Hadin Gwiwa

July 5, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan ‘Ƴan Nijeriya 2 A Afrika Ta Kudu

July 5, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Kafa Cibiyar Horar Da Ma’aikatan Jinya A Saliyo

July 5, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.