ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Cafke Yan Sudan Da Chadi 20 A Kano Bisa Shigo Wa Nijeria Ba Bisa Ka’ida Ba

by Abubakar Sulaiman
2 months ago
Kano

Jami’an NSCDC reshen Jihar Kano sun cafke wasu mutane 20 daga ƙasashen waje a yankin Danbare na Karamar Hukumar Kumbotso kan shigo wa Nijeriya ba bisa ka’ida ba.

Kwamandan reshen jihar, Mohammed Hassan-Agalama, ya bayyana haka ranar Talata a lokacin ganawa da manema labarai a Kano, inda ya ce waɗanda ake zargin sun fito ne daga Sudan, da Chadi, da Kamaru, da Nijar. “Daga cikin wadanda ake zargin, ɗaya daga Kamaru, ɗaya daga Nijar, 12 daga Sudan, da shida daga Chadi,” in ji Hassan-Agalama.

  • Kano Pillars Sun Yi Alƙawarin Sake Zage Damtse Bayan Rashin Nasarar Wasan Bayelsa
  • Kano Pillars Ta Lallasa Bendel Insurance A Kano

Ya bayyana cewa cafke su ya biyo bayan samun sahihan bayanan da kuma aikin haɗin gwiwa na jami’an NSCDC. Bincike na farko ya nuna cewa mafi yawansu ba su da sahihan takardun tafiya ko shaida ta ainihi, abin da ya haifar da damuwa game da ayyukansu a cikin jihar. An kama wayoyi Android guda 10 daga hannunsu.

ADVERTISEMENT

Hassan-Agalama ya kara da cewa, “Jami’an Corps suna ci gaba da bincike da tantance waɗanda ake zargin domin gano manufarsu da yiwuwar alaƙarsu da duk wasu ayyuka na laifi. Kuma an sanar da hukumomin da suka dace, kuma ana daukar matakai bisa doka.” Ya kuma jaddada jajircewar NSCDC wajen kare kadarorin ƙasa da tabbatar da tsaro a cikin gida, yana kira ga jama’a da su kasance masu lura da bayar da bayanai cikin lokaci.

Daya daga cikin wadanda aka kama, Idrisa Ila daga Jamhuriyar Nijar, ya shaida wa manema labarai cewa yana zaune a Kano tsawon shekaru uku yana gudanar da harkokin kasuwanci. Ya ce ya haɗu da wasu daga cikin wadanda aka kama ta Facebook, inda suka shirya tafiya zuwa Sudan ta Chadi, suna amfani da Nijeriya ne a matsayin wurin wucewa. “Sun ce ba su da isasshen kuɗi don ci gaba da tafiyarsu zuwa Sudan, shi ne suka yanke shawarar zama a Nijeriya na ɗan lokaci,” in ji Ila. Ya kara da cewa, da farko sun fara neman wuri zaman na ɗan lokaci, inda suka aiko masa da kuɗi don ya samo musu gida, amma daga baya adadin mutane ya karu fiye da yadda aka zata.

LABARAI MASU NASABA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Jama’ar a yankin sun fara yin shakku saboda yawan mazauna gidan da kuma rashin iya magana da Hausa ko Turanci, abin da ya sa suka sanar da hukumomi. Ila ya tabbatar da cewa yana da takardu sahihai, amma ba zai iya tabbatar da matsayin doka na sauran ba, wadanda suka zauna a Kano fiye da kwana 10 kafin a cafke su.

Kano
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2, Sun Yi Garkuwa Da 30 A Kogi
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci, Sun Kashe Wani Yaro A Kaduna
  • Abubakar Sulaiman
    Babachir Lawal Ya Fice Daga ADC, Ya Zargi Atiku Da Murɗe Zaben Fidda Gwani

MASU ALAKA

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
Labarai

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Kano

Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 4, Dukiyar Naira Biliyan 1 A Watan Maris

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.