Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano ta ce ta ceto rayukan mutane hudu tare da kare dukiyar da ta kai kimanin Naira biliyan 1 a cikin watan Maris na wannan shekara (2026).
Daraktan hukumar, Alhaji Sani Anas, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar, Alhaji Saminu Abdullahi, ya fitar ranar Laraba a Kano.
- Shugaban INEC Ya Yi Watsi Da Kiran Ya Yi Murabus, Ya Ce Wasa Da Hankali Ne Kawai
- Yanzu- Yanzu Atiku, Obi, Kwankwaso, Mark Da Sauransu Sun Jagoranci Zanga-Zanga Zuwa INEC
Sanarwar ta ce, mutane biyar sun rasa rayukansu sakamakon gobara, da hatsarin mota da kuma wasu hadurra da suka shafi fadawa ruwa, yayin da dukiyar da ta kai Naira miliyan 355 ta lalace sakamakon gobara a wannan lokaci.
Haka kuma, hukumar ta amsa kiran gaggawa guda bakwai tare da kuma karɓar kiran ƙarya guda uku daga mazauna jihar a cikin watan.
Hukumar ta bukaci masu shaguna da su sanya na’urorin gano gobara domin dakile aukuwar irin wadannan hadurra a nan gaba.















Discussion about this post