ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

by Sulaiman
1 hour ago
Kogi

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai mummunan hari ranar Laraba a al’ummar Iluke-Bunu da ke karamar hukumar Kabba-Bunu ta jihar Kogi, inda suka kashe mutane uku a wani yunkuri na sace daliban da ke rubuta jarabawar kammala sakandare ta WASSCE.

A cewar mazauna yankin, maharan dauke da manyan makamai, wadanda aka ce sun zo akan babura kusan 40 kuma sanye da kayan sojoji, sun afka wa al’ummar da misalin karfe 10:00 na safe, suna harbe-harbe ba kakkautawa kafin su nufi makarantar Sakandare ta Gwamnati, Iluke, inda ake zana jarabawar.

Shaidun gani da ido sun ce maharan sun tarwatsa taron jarabawar tare da kokarin tursasa wasu daliban zuwa cikin daji. Sai dai saurin daukar mataki da jami’an tsaro suka yi ya hana afkuwar wannan babbar masifar.

ADVERTISEMENT

A cikin wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ’yansandan jihar Kogi, ASP Saliu Oyiza Afusat, ta fitar, rundunar ta ce ta samu kiran gaggawa cewa wasu ’yan bindiga masu yawa sun mamaye makarantar da nufin yin garkuwa da dalibai da mazauna yankin.

Sanarwar ta ce babban jami’in kula da rundunar ’yansanda ta Kabba “A” ya gaggauta tattara jami’ansa tare da dakarun rundunar PMF da tawagogin musamman na rundunar da ke jihar, gami da sojoji da jami’an sa-kai da ke aiki a yankin.

LABARAI MASU NASABA

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

Haɗaɗɗiyar tawagar tsaron ta fafata da maharan a wani kazamin musayar wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa cikin dazukan da ke kusa da yankin.

Kogi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026
  • Sulaiman
    Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar
  • Sulaiman
    Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

MASU ALAKA

’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Manyan Labarai

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

June 10, 2026
Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026
Next Post
An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

An Bude Bikin Kasa Da Kasa Na Makon Nuna Fina-Finan Zane Mai Motsi Na Chongqing Na 2026

June 10, 2026
Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

Babban Yankin Kasar Sin Ta Soki ‘Yan Jam’iyyar DPP Na Taiwan Kan Yadda Suka Kaskantar Da Kansu Ga Kasashen Waje

June 10, 2026
An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

An Gudanar Da Taron Kirkire-Kirkire Na Duniya Na Kafafen Yada Labarai Karo Na Biyar

June 10, 2026
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

An Daƙile Yunƙurin Sace Ɗalibai Masu Zana Jarabawar WASSCE A Kogi

June 10, 2026
Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

Kamfanin Kasar Sin Ya Kammala Wani Muhimmin Titi A Fadar Mulkin Nijeriya

June 10, 2026
Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

Cudanyar Al’Adu Tana Tabbatar Da Kyakkyawar Makomar Sin Da Afirka 

June 10, 2026
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

Babu Makarantar Da Aka Kai Wa Hari A Neja – ‘Yansanda

June 10, 2026
Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

June 10, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

June 10, 2026
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

‘Yansanda Sun Kama Masu Satar Mutane, ‘Yan Fashi A Jigawa, Sun Ƙwato Makamai

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.