Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun kai mummunan hari ranar Laraba a al’ummar Iluke-Bunu da ke karamar hukumar Kabba-Bunu ta jihar Kogi, inda suka kashe mutane uku a wani yunkuri na sace daliban da ke rubuta jarabawar kammala sakandare ta WASSCE.
A cewar mazauna yankin, maharan dauke da manyan makamai, wadanda aka ce sun zo akan babura kusan 40 kuma sanye da kayan sojoji, sun afka wa al’ummar da misalin karfe 10:00 na safe, suna harbe-harbe ba kakkautawa kafin su nufi makarantar Sakandare ta Gwamnati, Iluke, inda ake zana jarabawar.
Shaidun gani da ido sun ce maharan sun tarwatsa taron jarabawar tare da kokarin tursasa wasu daliban zuwa cikin daji. Sai dai saurin daukar mataki da jami’an tsaro suka yi ya hana afkuwar wannan babbar masifar.
A cikin wata sanarwa da jami’ar hulda da jama’a ta rundunar ’yansandan jihar Kogi, ASP Saliu Oyiza Afusat, ta fitar, rundunar ta ce ta samu kiran gaggawa cewa wasu ’yan bindiga masu yawa sun mamaye makarantar da nufin yin garkuwa da dalibai da mazauna yankin.
Sanarwar ta ce babban jami’in kula da rundunar ’yansanda ta Kabba “A” ya gaggauta tattara jami’ansa tare da dakarun rundunar PMF da tawagogin musamman na rundunar da ke jihar, gami da sojoji da jami’an sa-kai da ke aiki a yankin.
Haɗaɗɗiyar tawagar tsaron ta fafata da maharan a wani kazamin musayar wuta, lamarin da ya tilasta musu tserewa zuwa cikin dazukan da ke kusa da yankin.















Discussion about this post