ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Dakatar Da “Wasan Matsorata” Da Jam’iyyun Siyasan Amurka Suke Yi Amma Damuwa Ta Dore

by CMG Hausa
3 years ago
Amurka

Bayan da majalisar wakilan kasar Amurka ta zartas da kudurin doka game da aikin kayyade basussuka da kasar za ta iya karba, kafofin watsa labaru na kasashe daban daban sun bayyana a jiya Alhamis cewa, batun nan tamkar “dakatar da yaki na wucin gadi ne, wanda ba a kawo karshensa ba tukuna”.

Kudurin ya dakatar da lokacin fara yin amfani na dokar kayyade yawan bashin da gwamnatin kasar Amurka za ta iya ci har zuwa farkon shekarar 2025, haka kuma an kayyade kudaden da za a kashe a cikin kasafin kudi na shekarar 2024 da ta 2025.

  • Jami’an Kasuwancin Sin Da Amurka Sun Amince Da Karfafa Muamala

Ga alama batun nan ya kau da damuwar wasu mutane. Sai dai ko da majalisar dattawa ta kasar Amurka ta amince da kudurin a nan gaba, kuma shugaban kasar shi ma ya sanya masa hannu, shin da gaske ne za a iya warware matsalar ta wannan dabara? Shin da gaske ne Amurka din da sauran sassan duniya suna cikin wani yanayi mai tsaro yanzu?

ADVERTISEMENT

A halin yanzu, a kasuwannin takardun bashi na kasa da kasa an fi samun takardun shaidar bashin da ake bin gwamnatin kasar Amurka. Saboda haka idan gwamantin kasar Amurka ta kasa biyan bashin, to, ita kasar da sauran kasashe daban daban za su shiga cikin mawuyacin hali. Don tinkarar wannan yanayin da za a iya samu, kasar Amurka ta dauki wannan dabara: wato a dakatar da lokacin fara aiki na dokar kayyade bashin da za ta iya karba da tsawon shekaru biyu. Ko da yake wannan dabara ta dakatar da matsala kawai, maimakon warware ta daga tushe. Ban da haka kuma za ta sanya bashin da kasar Amurka ta ci dinga karuwa.

A matsayinta na kasa mafi tasirin tattalin arziki a duniya, muhimman alkaluman ma’aunin tattalin arzikin kasar Amurka na ci gaba da raguwa, kana ana fuskantar babban hadarin samun koma bayan tattalin arzikin kasar, yayin da dimbin bankunan kasar ke fuskantar mawuyacin hali, lamarin da ya haifar da wani yanayi na rashin tabbas ga sauran sassan duniya.

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Yanzu, rikicin bashi na Amurka, wanda aka kwashe watanni da dama ana tinkararsa, yana ci gaba da haifar da matsaloli a kasuwannin kasa da kasa. Daga cikin wannan “wasan matsorata” da jam’iyyun siyasan kasar Amurka suke yi, wanda ba a san lokacin da za a kawo karshensa daga tushe ba, wani ilimin da mutanen duniya suka samu shi ne, kasar Amurka ce ke haifar da babban hadari ga tattalin arzikin duniya.(Safiyah Ma)

Amurka
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 16, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Next Post
Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

Yadda Aka Kammala Gasar Firimiya Ta Bana

LABARAI MASU NASABA

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

June 17, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Mata Ta Hallaka Mijinta Da Wuƙa Watanni Biyu Bayan Aure A Kano

June 17, 2026
An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

An Kaddamar Da Wani Kwas Na Horar Da Kwararru Kan Killace Kananan Makamai Na Sin Da MDD Da Afirka 

June 16, 2026
Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

Mataimakin Firaministan Sin Zai Halarci Babban Taron Shugabanni Game Da Barkewar Cutar Ebola

June 16, 2026
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Dakatar Da INEC Game Da Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu

June 16, 2026
Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

Tattalin Arzikin Sin Ya Tafiya Cikin Kwanciyar Hankali

June 16, 2026
Gaza

Farashin Mai Ya Faɗi Ƙasa Da Dala 80 Bayan cimma Yarjejeniyar Amurka Da Iran

June 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Myanmar

June 16, 2026
Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

Tinubu Ya Kaddamar Da Katafaren Gidajen Alƙalan Kotun Ɗaukaka Ƙara A Abuja

June 16, 2026
Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

Kasar Sin Na Samar Da Managarcin Yanayi Na Bunkasa Kirkire-kirkire Ga Masana’antun Kasa Da Kasa

June 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.