Ofishin jakadancin Sin a Najeriya da gidan rediyon muryar Najeriya (VON), sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a jiya Litinin 18 ga watan nan, inda suka fara gabatar da shirin koyar da harshen Sinanci mai suna “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” a hukumance.
Ofishin jakadancin Sin a Najeriya da kafar VON sun shirya wannan shiri ne tare, da kuma hadin gwiwar cibiyar al’adun Sin a Najeriya, don watsa shirin ga kasashen Afirka daban-daban. Ana tsara watsa shiri guda daya a kowane mako, kowane shiri zai dauki kusan mintuna 15, inda za a ba da labarin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka.
Jakadan Sin a Najeriya Yu Dunhai ya yi fatan cewa, karin ‘yan kasashen Afirka za su fahimci Sin ta hanyar wannan shiri mai taken “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya”, kuma za su zama masu inganta abotar Sin da Afirka, kuma masu shiga a dama da su cikin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka, kana masu cin gajiyar wannan abota.
Daraktan gidan rediyon muryar Najeriya Jibrin Ndace, ya bayyana cewa, fara gabatar da shirin “gadar abota tsakanin Sin da Najeriya” zai samar da dandamali ga bangarorin biyu, na kara fahimtar juna ta hanyar koyar da harshe da musayar al’adu. (Amina Xu)















Discussion about this post