Jam’iyyar ADC a Jihar Nasarawa ta kammala aikin tantancewa tare da amincewa da duk masu neman takara daga kujerun Majalisar Dattawa, Majalisar Wakilai ta Tarayya da kuma Majalisar Dokokin Jiha, yayin da jam’iyyar ke shirin gudanar da zaɓen fidda gwani.
Da yake jawabi ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala aikin a ranar Litinin, shugaban kwamitin riƙo na jam’iyyar a jihar, Chief Michael Abdul, ya bayyana cewa aikin ya gudana cikin kwanciyar hankali ba tare da wata matsala ba, inda aka kula da duk masu neman takara da suka miƙa fom da takardunsu.
Ya ce:“Da na isa sakatariyar jam’iyyar, na gana da shugaban riƙo, Barr. Paul Magaji Aji, wanda ya raka ni wajen shugaban kwamitin tantancewa da ya fito daga Jihar Filato.
“Na tattauna sosai da shugaban da sauran mambobin kwamitin tantancewar, kuma sun shaida min cewa sun kammala aikinsu.
“Sun tantance duk masu neman takara daga Jihar Nasarawa a jam’iyyar ADC da ke neman kujerun Majalisar Dattawa, Majalisar Wakilai ta Tarayya da kuma Majalisar Dokokin Jiha.”
Chief Michael Abdul, wanda tsohon mataimakin gwamnan Jihar Nasarawa ne, ya ce yadda aikin ya gudana lafiya ba tare da an kai wata ƙara gaban kwamitin ɗaukaka ƙara na jam’iyyar ba, hakan alama ce cewa jam’iyyar ta shirya tsaf domin karɓar jagoranci a jihar a shekarar 2027 da ma bayan haka.















Discussion about this post