ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Gudanar Da Taro Kan “Ci Gaba Mai Inganci Da Nasarorin Da Aka Samu A Jihar Xinjiang” A Taro Na 51 Na Kwamitin Kare Hakkin Dan Adam Na MDD

by CMG Hausa
4 years ago
MDD

An gudanar da taron gefen kasar Sin kan “ci gaba mai inganci da nasarorin da aka samu a jihar Xinjiang” a taro karo na 51 na kwamitin kare hakkin dan Adam na MDD a birnin Bole dake jihar Xinjiang ta kasar.

Yayin taron da aka yi ta kafar bidiyo da kuma ido da ido a jiya, masana da malamai fiye da goma na gida da waje da wasu wakilan jama’ar jihar Xinjiang da wakilan daliban kasashen waje da ke karatu a kasar Sin, sun yi tattaunawa mai zurfi kan sauye-sauyen da aka samu a jihar Xinjiang sakamakon ci gaba mai inganci, da kuma nasarorin da aka samu a fannin kare hakkin bil’adama.

  • Kasar Sin Ta Bankado Karin Shaidu Game Da Kutsen Yanar Gizo Da Amurka Ta Yi Mata

Hussein Ibrahim Morsy, shugaban kwalejin koyar da harsuna da fassara na jami’ar kimiyya da fasaha ta Masar, kuma farfesa a sashen koyar da Sinanci na jami’ar Ain Shams, yana ganin cewa, gwamnatin kasar Sin tana mai da hankali sosai kan aikin ba da ilmi ga kananan kabilu da yankunan da ‘yan kananan kabilu ke taruwa, kuma ta dauki kwararan matakai na kare hakkin kananan kabilu wajen samun ilimi, da kyautata halin yankunan da ‘yan kananan kabilu ke taruwa da jama’ar dake zaune a yankunan da inganta zaman rayuwar jama’a a yankunan, kuma an samu manyan nasarori.

ADVERTISEMENT

Ye Suya, wata daliba ‘yar Najeriya dake karatu a jami’ar horar da malamai ta Zhejiang, da Ou Jingya, daliba ‘yar kasar Mozambique, sun ziyarci jihar Xinjiang a baya-bayan nan, kuma sun bayyana cewa, hadin kan al’ummar yankin da kokarin da gwamnatin ke yi na karewa da kuma gadon abubuwan tarihi na al’adu da ake gada daga kakanni kakanni, sun burge su kwarai da gaske. A ganinsu, Xinjiang “wuri ne mai cike da karfi”.

Shi kuwa babban darektan cibiyar binciken hakkin dan Adam ta jami’ar koyon dokokin shari’a ta arewa maso yammacin kasar Sin, Chang An cewa ya yi, yadda Amurka da kasashen yammacin duniya ke yayata batutuwan da suka shafi hakkin dan Adam a jihar Xinjiang, hakika, alama ce ta zahiri ta siyasantar da hakkin bil’adama da amfani da batun don cimma burinsu.

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Kana ya lalata albarkatun jama’ar kasa da kasa a fannin kare hakkin bil’adama don nuna danniya ko babakere, lamarin da ya sabawa manufar ci gaban kare hakkin bil’adama a duniya. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

MDD
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Bayyana Imanin Tabbatar Da Samun Ci Gaban Cinikin Waje A Karshen Rabin Shekarar Bana

Ma'aikatar Kasuwancin Sin Ta Bayyana Imanin Tabbatar Da Samun Ci Gaban Cinikin Waje A Karshen Rabin Shekarar Bana

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.