An gudanar da taro na musamman game da “fitar da kaya zuwa Sin” a Alkahira, babban birnin kasar Masar a ranar 17 ga watan nan. Kamfanonin Sin da Masar sun sanya hannu kan yarjejeniyoyin ciniki da dama a yayin taron, inda jimillar darajar kwangilolin ta kai kusan dala miliyan 170.
Babban direktan sashen Asiya na ma’aikatar zuba jari da cinikayyar waje ta Masar Sayed Fouad ya gode wa bangaren Sin bisa shirya taron na musamman na “fitar da kaya zuwa Sin” a kasar ta Masar. Ya bayyana cewa, bangaren Masar yana fatan kara hadin gwiwa mai dorewa tare da bangaren Sin, da karfafa musayar kasuwanci da tattalin arziki, da kuma ciyar da dangantakar kasuwanci da tattalin arziki tsakanin kasashen biyu gaba.
Jami’in sashen cinikayyar shige da fice na ma’aikatar kasuwanci ta Sin Chang Hui ya bayyana cewa, taron shi ne bikin farko na jerin bukukuwan “fitar da kaya zuwa Sin” da za a gudanar a kasashen Afirka.
Gudanar da jerin bukukuwan wani sabon mataki ne na Sin da nufin more fa’idodin ci gaba da damammakin kasar Sin tare da abokan cinikinta na duniya, da kuma kare tsarin kasuwanci tsakanin mabambantan bangarori da ciniki cikin ‘yanci.Bisa labarin da aka bayar, an c, wakilan siyasa da ‘yan kasuwa daga kasashen biyu kimanin 170 sun halarci taron. (Amina Xu)














