Rasha ta gargadi Birtaniya kan abin da ta kira “sakamako” bayan gwamnatin Birtaniya ta tabbatar da cewa an yi amfani da jiragen yaki marasa matuka da aka ƙera a Birtaniya wajen kai hare-haren baya-bayan nan na kasar Ukraine kan wuraren soji da masana’antu a cikin ƙasar Rasha.
Ofishin Jakadancin Rasha da ke Birtaniya ya zargi London da kalaman ƙara zafafa rikicin Ukraine, yana mai cewa yayin da Birtaniya ke ƙara zurfafa shiga cikin rikicin, haka, sakamakon aikinta zai ƙaru.
Ofishin jakadancin ya kuma ce “matakan da London ke ɗauka babu makawa za su haifar da sakamako wanda za ta fuskanta,” sai dai bai bayyana irin matakin da Moscow za ta iya ɗauka ba.
Gargadin ya biyo bayan jerin hare-haren jiragen yaki marasa matuka da Ukraine ta kai cikin yankunan Rasha, ciki har da hare-haren da suka shafi Moscow, matatun mai da kuma wuraren ajiyar kayayyaki na kamfanin sayar da kaya ta intanet na Wildberries.
A nata ɓangaren, Ma’aikatar Tsaron Birtaniya ta ce ƙasar za ta ci gaba da tsayawa “kafada da kafada” da Ukraine, duk da gargadin da Rasha ta yi.














