An gudanar da taron tattaunawa na kasa da kasa na magadan gari na shekarar nan ta 2026 a birnin Beijing fadar mulkin kasar Sin.
Taron wanda majalisar gudanarwar kasar Sin ta shirya tsakanin jiya Talata zuwa yau Laraba, ya hallara magadan gari, da wakilan wasu birane sama da 30, daga kasashen Afirka shida, da suka hada da na Morocco, da Seychelles, da Tunisia, da Senegal, da kuma membobi masu wakiltar kungiyar gamayyar hukumomin yawon bude ido na biranen duniya.Mahalarta taron sun yi musaya mai zurfi, da tattaunawa game da jigon taron na wannan karo, wato “Karfafa musaya tsakanin mabanbantan wayewar kai da koyi da juna, da ci gaba da yaukaka kawancen gargajiya tsakanin Sin da kasashen Afirka”, kana sun yi hadin gwiwar lalubo hanyar bunkasa musayar al’adu tsakanin al’ummu, da kuma hadin gwiwar birane tsakanin Sin da kasashen Afirka. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post