Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen Sin Mao Ning, ta ce babu wata makoma ga duk wani wanda ya hada kai da ’yan awaren yankin Taiwan, kuma hakan zai haifar da rasa damar samun ci gaba, da kuma ware kai daga sauran al’ummomin duniya.Mao ta bayyana haka ne yayin taron manema labarai na yau da kullun da ake gudanarwa na yau Laraba, lokacin da take mayar da martani ga ziyarar aikin ’yan awaren yankin Taiwan a kasar Swaziland a kwanan nan.
Dangane da dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da EU kuwa, Mao ta ce jigon wannan dangantaka shi ne cimma moriyar juna, da cimma nasara tare.
Ta ce Sin na fatan EU za ta bi ka’idodin tattalin arziki na kasuwa, kamar ciniki cikin ’yanci, da gogayya cikin adalci, da hadin gwiwa a bude, da kuma guje wa matakan ra’ayin ba da kariya.Bugu da kari, dangane da halin da ake ciki yanzu haka tsakanin Amurka da Iran, Mao ta ce Sin ta damu matuka.
Ta ce yaki bai dace da muradun kowane bangare ba. Don haka ana fatan dukkanin bangarorin da abin ya shafa za su daraja damar samun zaman lafiya, kuma su ci gaba da warware takaddama ta hanyar siyasa da diflomasiyya. (Safiyah Ma)















Discussion about this post