Da misalin karfe 10 saura mintuna biyar na safiyar yau Talata, daya ga watan Satumba, aka gudanar da taron makokin mutanen da suka rasu sakamakon ibtila’in zabtarewar kasa da ya auku a yankin Gyirong. An gudanar da taron ne a ofishin hukumar lura da tsaron al’umma reshen tashar ruwa ta Shigatse dake jihar Xizang mai cin gashin kai ta kasar Sin.
Har ila yau, an gudanar da makamancin wannan taro a muhimman wuraren da aka yi aikin ceton wadanda ibtila’in ya rutsa da su, da kuma hanyoyin da ake gyarawa bayan lalacewarsu sakamakon aukuwar bala’in. Ma’aikata daga sassa daban daban, da jami’an wurin da mazauna yankunan sun halarci taron makokin.
Ma’aikatan ceto na amfani da manyan injuna a aikin da suke yi ba dare ba rana, domin sake bude babbar hanyar zuwa kafar Gyirong da ibtila’in zabtarewar kasa ya shafa, a lardin Xizang da ke kudu maso yammacin Sin, domin saukaka shigar kayayyakin aiki da ma’aikata da sauran kayayyakin bukata yankin.
Ma’aikatan ceto daga rukunin China Anneg, sun ce zuwa jiya Litinin da rana, an samu damar gyara kilomita 1.1 na babbar hanyar G216, inda suka ce suna kokarin gaggauta farfado da hanyar mai matukar muhimmanci.
A cewar gwamnatin yankin, wata mummunar zabtarewar laka da rugujewar kankara daga kan tsauni ta haifar a kasar Nepal, ta shafi kafar Gyirong a ranar 26 ga watan Augusta, inda zuwa karfe 6 na yammacin ranar Asabar, ta yi sanadin rayuka 16 da batar wasu mutane 546 a kafar da ke kan iyakar Sin.
Ibtila’in ya lalata gine-gine da hanyar wutar lantarki da wani bangare na titin G216, lamarin da ya kawo cikas ga ayyukan agaji da na ceto. (Saminu Alhassan+Fa’iza Mustapha)














