An kaddamar da ginin katafariyar tashar ruwa ta zamani domin ayyukan kiwon kifi a kasar Saliyo, aikin da kasar Sin ta samar da tallafin gudanar da shi.
Ana sa ran aikin zai kasance babban mataki a yunkurin Saliyo na zamanantar da harkar kiwon kafi, tare da bunkasa tattalin arziki marar gurbata yanayi.
A ranar Alhamis ne aka kaddamar da aikin, na hadin gwiwa tsakanin Sin da gwamnatin Saliyo, a kauyen Black Johnson dake yankin karkarar yammacin kasar, mai nisan kilomita kusan 35 kudu da birnin Freetown fadar mulkin kasar ta Saliyo.
Cikin jawabinsa na bikin kaddamar da aikin, shugaban kasar Saliyo Julius Maada Bio, ya ce tashar ruwan ta kiwon kifi za ta taimakawa Saliyo da damar cin gajiyar fannin tattalin arziki marar gurbata yanayi, da rage asarar kusan dalar Amurka miliyan 42 duk shekara, wanda kasar ke yi a fannin hada-hadar kiwon kifi, tare kuma da samar da guraben ayyukan yi. (Mai fassara: Saminu Alhassan)















Discussion about this post