Tawagar wakilai ta dindindin ta kasar Sin dake MDD ta shirya taron kaddamar da kungiyar abokai ta tafiyar da harkokin duniya a hedkwatar MDD dake birnin New York, lamarin da ya tabbatar da kafuwar kungiyar a hukumance. Zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Fu Cong ne ya jagoranci wannan taro, wanda ya samu mahalarta daga kasashe kusan 40 da suka hadu suka kafa kungiyar.
Fu Cong ya bayyana cewa, bisa jagorancin shawarar tafiyar da harkokin duniya ne kasar Sin ta ba da shawarar kafa kungiyar abokai ta tafiyar da harkokin duniya, da nufin aiki tare da bangarori daban daban don karfafa cudanya da hadin gwiwa kan manyan batutuwan da suka shafi harkokin duniya, da inganta kafa wani tsarin tafiyar da harkokin duniya mai adalci yadda ya kamata. Fu Cong ya kara da cewa, kasarsa na fatan hada hannu da mambobin kungiyar don kayutata tsarin kungiyar, da ma zurfafa mu’amala da hadin kai, da kuma ba da gudunmowa ga yin kwaskwarima da kyautata ayyukan tafiyar da harkokin duniya.
Wakilan kasashe mahalarta taron sun yi jawabi, inda suka yi lale marhabin da kafuwar kungiyar. Dukkansu sun yaba wa rawar da kasar Sin ta taka wajen jagorantar tafiyar da harkokin duniya, da kuma bayyana fatansu na ganin kungiyar ta karfafa yin cudanya kan manufofi da zurfafa hakikanin hadin kai, da kara azama kan kiyaye ra’ayin cudanyar bangarori da dama, da yin kwaskwarima da gina tsarin tafiyar da harkokin duniya. (Mai fassara Bilkisu Xin)














