Kwamitin Majalisar Wakilai Kan Yaki da Cin Hanci da Rashawa ya sake jaddada kudirinsa na aiwatar da ayyukansa wadanda za su tallafawa matasan Nijeriya don bayar da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban kasa.
Shugaban Kwamitin, Moshood Akiolu, ya jaddada wannan kudirin a ranar Laraba a wani taron bikin Ranar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Duniya ta 2025 a Abuja.
- An Kafa Kungiyar Abokai Ta Tafiyar Da Harkokin Duniya A Hedkwatar MDD
- Gwamnati Ta Yaƙi Talauci, Rashin Tsaro, ’Yancin Jama’a Don A Hana Aukuwar Juyin Mulki A Nijeriya – Falana
Akiolu ya kara da cewa, Majalisar Wakilai ta 10, karkashin jagorancin Kakakin Majalisa Tajudeen Abbas, tana kara himma wajen fayyace ayyukanta a fili, karfafa cibiyoyin shari’a, da kuma fadada shirye-shiryen wayar da kan jama’a don ganowa, da kin almundahana da kuma bayar da rahoton ayyukan cin hanci da rashawa.
A cewarsa, “Majalisar tana aiki don inganta gaskiya, karfafa tsarin shari’a, wayar da kan al’umma da kuma tallafawa matasa don tsayawa tsayin-daka wajen yakar duk ayyukan cin hanci da rashawa da kuma bayar da rahoto akansu.”














