An kama tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji, a Filin Jirgin Saman Akanu Ibiam da ke Enugu.
Jaridar Premium Times ta ruwaito ce an kama Nnaji ne da safiyar ranar Laraba yayin da yake shirin zuwa Abuja.
Ana sa ran za a miƙa shi ga Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) domin ci gaba da bincike.
An kama shi ne bayan wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa ICPC umarnin kama shi a watan Yuni bisa zargin gabatar da takardun shaidar karatu na ƙarya.
Kotun ta kuma bai wa hukumar izinin ayyana shi a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo idan ya ƙi amsa gayyata.
ICPC ta shaida wa kotun cewa Nnaji ya yi watsi da gayyatar da aka yi masa domin amsa tambayoyi kan zargin.
Ana zargin Nnaji da gabatar da takardun digiri na Jami’ar Nsukka (UNN) da kuma takardar kammala NYSC na ƙarya lokacin da aka naɗa shi minista a shekarar 2023.
Nnaji ya yi murabus daga muƙaminsa a watan Oktoban 2025, inda ya ce ya sauka ne domin bin doka da ƙa’ida, ba wai saboda ya amince da zargin da ake masa ba.
Kafin a kama shi, Nnaji ya musanta zargin tare da ƙalubalantar umarnin kotun a Kotun Ɗaukaka Ƙara.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sanarwa a hukumance daga Nnaji ko kuma ICPC kan kama shi.














