Aƙalla mutane 19 ake zargin sun rasa rayukansu, yayin da wasu da dama suka jikkata, bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari ƙauyen Kawel da ke yankin Mushere a Ƙaramar Hukumar Bokkos a Jihar Filato a daren ranar Lahadi.
Mazauna yankin sun ce maharan sun shiga ƙauyen ne da misalin karfe 11:40 na dare, yayin da mutane ke barci, suka fara harbe-harbe, lamarin da ya tilasta mazauna ƙauyen gudu domin tsira da rayukansu.
Wani mazaunin yankin ya ce maharan sun riƙa yawo a ƙauyen suna harbi ba ƙaƙkautawa, inda ya tabbatar da mutuwar sama da mutane 19, yayin da wasu da dama suka samu raunuka.
Shugaban matasan Bokkos, Christopher Luka, ya tabbatar da harin, inda ya ce an sanar da shi da misalin karfe 12 na dare, sannan ya hanzarta sanar da jami’an tsaro.
Ya ce jami’an tsaro sun tabbatar masa da cewa sun samu labarin lamarin kuma suna kan hanyar zuwa wajen da abin ya faru.
Shugabannin al’umma sun bayyana harin a matsayin abun firgici tare da kira ga gwamnati da hukumomin tsaro da su kara ƙaimi wajen kare kauyuka da ke fuskantar irin waɗannan hare-hare.
Wannan harin ya faru ne kwanaki kaɗan bayan wani hari makamancin irinsa da ya yi sanadin mutuwar wani shugaba al’umma a yankin, lamarin da ya ƙara tayar da hankali kan matsalar tsaro a Bokkos da kewayenta.















Discussion about this post