Dakarun rundunar haɗin gwiwa ta Operation Hadin Kai a Arewa Maso Gabas sun ceto mutane 47, yawancinsu mata da ƙananan yara, daga hannun ‘yan ta’addar ISWAP a Kangarwa, Ƙaramar Hukumar Kukawa a Jihar Borno.
An gudanar da aikin ceto ne a ranar 20 ga watan Yuni, 2026, a lokacin wani farmaki a yankin Tafkin Chadi.
Rahoton sojoji ya ce matsin lamba daga hare-haren ƙasa da na sama ya tilasta ‘yan ta’addar barin wuraren da suke, wanda hakan ya ba da damar ceto mutanen da aka yi garkuwa da su.
Yanzu haka waɗanda aka ceto na samun kulawa a wani waje mai tsaro tare da shirye-shiryen mayar da su wajen ‘yan uwansu.
Hukumomin soji sun ce wannan aikin wani ɓangare ne na ƙoƙarin rage ƙarfin ‘yan ta’adda da kuma kuɓutar da fararen hular da aka sace.
Sun kuma jaddada cewa za su ci gaba da kai hare-hare har sai an samu cikakken zaman lafiya a yankin Arewa maso Gabas.















Discussion about this post