Akalla mutum biyu daga cikin gungun ’yan bindigar da ke addabar mazauna Babban Birnin Tarayya (FCT) Abuja sun mutu bayan jami’an tsaro sun harbe su.
Kwamishinan ’yansandan FCT, CP Ahmed Mohammed Sanusi, ne ya bayyana hakan ga manema labarai a hedikwatar rundunar ranar Laraba, inda ya ce shi da kansa ya jagoranci aikin da ya kai ga kashe ’yan bindigar.
An bi sawun ‘yan bindigar ne bayan sace wasu mazauna garin Paze da ke yankin Byazhin a karamar hukumar Bwari a makon da ya gabata.
A baya, Daily Trust ta ruwaito cewa an yi garkuwa da mutum biyar ciki har da wani fasto, yayin da wani dan kungiyar sa-kai mai suna Shuaibu Yerima ya rasa ransa bayan ’yan bindiga sun kai hari garin Paze ranar Alhamis.
A cewar kwamishinan ’yansandan, an kubutar da mutanen da aka sace ne a yayin wani samame da hadin gwiwar jami’an sashen yaki da garkuwa da mutane, rundunar Intelligence Response Team (IRT), da Kubwa Area Command, tare da hadin gwiwar mafarauta da jami’an tsaro na sa-kai suka gudanar.
Ya ce da misalin karfe 9:00 na dare ranar Talata ne ya jagoranci hadaddiyar tawagar tsaron wajen kaddamar da wani gagarumin aikin bincike, sintiri da ceto a yankunan Paze da Byazhin.Rahotanni sun ce aikin ya kai ga kama wasu da ake zargi masu suna Icheh Mohammadu da Abubakar Usman, yayin da sauran ‘yan bindigar suka tsere zuwa tsaunukan da ke kusa da yankin.














Discussion about this post