Mataimakin wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Sun Lei, ya yi jawabi a taron kwamitin sulhu kan batun Afirka ta tsakiya a jiya Talata. A jawabin nasa, Sun ya ce kasar Sin na kira ga kasashen yankin da su ciyar da tsarin siyasa mai hade dukkanin sassa gaba, da karfafa hadin gwiwa wajen yaki da ta’addanci, da kuma inganta ikon samun ci gaba da karfin kansu.
Ya ce kamata ya yi al’ummun kasa da kasa su mutunta ikon mulkin kai na kasashen yankin da kuma jagorancinsu, su goyi bayan dukkan kasashe wajen ciyar da tsarin zaman lafiya da siyasa gaba, ta hanyar tattaunawa da shawarwari, da kuma taimakawa kasashen yankin wajen inganta karfin yaki da ta’addanci da kuma kula da iyakoki.
Sun Lei ya bayyana cewa, bangaren Sin yana goyon bayan kasashe masu tasowa, a fannin magance matsalolin Afirka ta hanyoyin kashin kansu, kuma yana fatan yin hadin kai da al’ummar kasa da kasa, wajen goyon bayan kasashen yankin, ta yadda za su bi sabuwar hanyar samun ci gaba ta dogaro da kai, da kuma bayar da babbar gudummawa wajen ciyar da Afirka ta tsakiya gaba, zuwa cimma dorewar zaman lafiya da wadata. (Amina Xu)














Discussion about this post