Ranar 12 ga watan Satumba, rana ce ta hadin gwiwar kasashe masu tasowa ta duniya ta MDD. A ranar bikin wato jiya Asabar, sashen wakilan hukumar raya kasa da kasa ta MDD wato UNDP dake Sin, ya fitar da bayanan baya-bayan nan game da ci gaban aikin raya hadin gwiwar kasashe masu tasowa, wanda hukumar da bangaren kasar Sin ke gudanarwa tare a birnin Hangzhou na Sin.
A karkashin goyon bayan jarin da bangaren Sin ta bayar kamar asusun ci gaban kasa da kasa da na hadin gwiwar kasashe masu tasowa, tun daga shekarar 2011, UNDP ta yi aiki tare da gwamnatin Sin, inda suka gudanar da ayyuka 39 kan hadin gwiwar kasashe masu tasowa, kamar sake gina gidaje da makarantu a yankunan da ibtila’in yanayi ya shafa don taimaka wa yara su koma makaranta, da aiwatar da ayyukan horar da ma’aikata don ba da tallafi ga iyalai masu talauci, da kuma taimaka wa kasashe masu tasowa su samu ci gaba mai dorewa bisa amfani da fasahohi masu kiyaye muhalli. Dangane da sabbin bayanan da UNDP ta fitar a ranar, an aiwatar da jerin ayyuka “kanana amma masu tasiri” a kasashe 26, wadanda suka amfanar da mutane kusan miliyan 20.
A nasa bangare, Stefan Liller, wakilin UNDP a Sin, ya bayyana cewa ta hanyar hadin gwiwa kadai ne kasashe za su iya tunkarar dimbin kalubalen duniya tare, wadanda babu wata kasa guda daya da za ta iya magance su ita kadai. Abin lura a nan shi ne, ana ganin wannan ruhi na hadin gwiwa a fannin yadda Sin ta kara gudanar da ayyuka domin bunkasa ci gaban duniya. (Safiyah Ma)














