An gudanar da taron cika shekaru 50 da fara ba da agajin jinya na tawagar likitoci ta kasar Sin dake karkashin jagorancin jihar kabilar Zhuang ta Guangxi mai cin gashin kanta a kasar Nijar, a babban asibitin Nijar dake birnin Yamai jiya Laraba.
Jakadan Sin dake Nijar, Lv Guijun, da sakataren reshen kwamitin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban kwamitin kiwon lafiya na jihar Guangxi, Du Zhenzong, tare da tawagar kiwon lafiya ta Guangxi, da ministan kiwon lafiya na jamhuriyar Nijar kanar Garba Hakimi, da shugaban babban asibitin Nijar Mamane Daou, da sauran wakilan ’yan siyasa da ma wakilan likitoci daga Nijar, da ma’aikatan WHO dake ofishin Nijar, da kuma mambobin tawagar ba da agajin jinya ta Sin da aka tura zuwa Nijer karo na 25, sun halarci taron.
Malam Hakimi ya mika godiya ga bangaren Sin a madadin gwamnatin Nijar da al’ummar kasar. Ya ce, hadin gwiwar kiwon lafiya tsakanin Nijar da Sin, kyakkyawar shaida ce ga abokantakar kasashen biyu. Tawagar ba da agajin jinya ta Sin ta bayar da babbar gudummawa ga bangaren Nijar a fannonin gudanar da hidimomin kiwon lafiya, da musayar fasahohi da kuma horar da jami’an jinya.
A watan Janairun shekarar 1976, tawagar ba da agajin jinya ta Sin da ta fito daga jihar Guangxi ta isa jamhuriyar Nijar. Kawo yanzu, an tura jimillar tawagogi 25 da suka kunshi masu aikin jinya 786 zuwa Nijar, kuma a halin yanzu masu ba da agajin jinya guda 30 daga tawaga ta 25 suna gudanar da aiki a jamhuriyar Nijar. (Safiyah Ma)















Discussion about this post