An yi wani taron kara wa juna sani na kasa da kasa mai taken “Tabbatar da tsaro cikin hadin-gwiwa: Sin da Afirka na daukar matakai tare”, jiya Alhamis 4 ga watan Disamba a hedikwatar kungiyar tarayyar Afirka wato AU da ke Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha. Taron ya samu halartar jami’an diflomasiyya na kasa da kasa, gami da wakilan AU da Majalisar Dinkin Duniya da kungiyoyin kwararru da kafafen yada labarai na kasashe daban-daban.
Shugabar sashin kula da harkokin tsaro na ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Wang Lixin ta gabatar da jawabi cewa, duniya na fuskantar yanayi mai sarkakiya a halin yanzu, inda kokarin kasar Sin na aiwatar da shirin raya kasa na shekaru biyar karo na 15 ke haifar da manyan damarmaki ga duk duniya. Ta ce ya dace Sin da Afirka su kara hada kai don aiwatar da shawarar tabbatar da tsaro a duniya, da shawarar inganta tsarin shugabancin duniya, da taimakawa ga zamanantar da harkokin zaman lafiya da tsaro, da kyautata tsarin shugabancin duniya, da kara raya al’ummomin Sin da Afirka masu kyakkyawar makoma ta bai daya, da zummar bayar da karin gudummawa ga sha’anin wanzar da zaman lafiya da samar da ci gaba a duniya.
A nasa bangaren kuwa, mataimakin darektan ofishin shugaban kwamitin kungiyar AU, Moussa Mohamed Omar ya bayyana cewa, matsalolin tsaro da nahiyar Afirka ke fuskanta yanzu, ba matsaloli ne da ke shafar wannan shiyya kawai ba, ciki har da ta’addanci, da yaduwar makamai ta hanyar da ba ta dace ba, da kuma sauyin yanayi. Shawarar inganta tsaro ta duniya na tsayawa kan aiwatar da ra’ayin tsaro mai dorewa kuma cikin hadin-gwiwa, al’amarin da ya dace da matsayar Afirka.
Tawagar jami’an diflomasiyyar kasar Sin da ke AU, da kwamitin AU, gami da ofishin MDD da ke AU din, su ne suka dauki nauyin shirya taron, inda mahalarta ke ganin cewa, shawarar kasar Sin ta bullo da dabarun kasar a fannin shawo kan kalubalen da Afirka, har ma da duk duniya ke fuskanta, kana, kasar Sin tana taka muhimmiyar rawa ga tabbatar da tsaro da samar da ci gaba a Afirka, kuma karfafa hadin-gwiwar Sin da Afirka zai kara sanya kuzari ga duk duniya. (Murtala Zhang)














