Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, , ya nuna damuwa kan ci gaba da tsare tsohon gwamnan Jihar Kaduna, yana mai cewa sharuɗan beli bai kamata su zama hanyar hukunta mutum kafin kotu ta yanke hukunci a kansa ba.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, Atiku ya ce beli na da muhimmanci wajen kare haƙƙin wanda ake tuhuma, domin doka ta ɗauki mutum a matsayin marar laifi har sai an tabbatar da laifinsa a kotu.
Ya yi tambaya kan sharuɗan belin da aka gindaya wa El-Rufai, waɗanda suka haɗa da gabatar da wani ma’aikacin gwamnatin tarayya mai matsayi na 17 da ke aiki a halin yanzu, wanda kuma yake da gida a Maitama ko Asokoro a Abuja, tare da wasu ƙarin sharuɗa.
A cewarsa, irin waɗannan sharuɗa suna da wahalar cikawa ga yawancin ’yan Nijeriya, kuma suna haifar da tambaya ko da gaske an yi niyyar bayar da beli ne ko kuma hana wanda ake tuhuma.
Atiku ya ce batun ba iya El-Rufai kaɗai ya shafa ba domin yana da tasiri ga duk wani ɗan ƙasa da zai iya fuskantar irin wannan hali a gaba.
Ya jaddada cewa ya kamata tsarin shari’a ya kasance mai adalci da sauƙin samu ga kowa, ba tare da la’akari da matsayinsa ko ra’ayinsa na siyasa ba.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya kuma ce aikin kotu shi ne tabbatar da adalci da kare ’yancin jama’a, ba wai amfani da sharuɗan beli wajen ci gaba da tsare mutum ba.
Ya yi gargaɗin cewa idan sharuɗan beli suka zama kasance ba za a iya cikawa ba, hakan na nufin an hana mutum samun beli, wanda zai iya tauye haƙƙoƙin da kundin tsarin mulki ya tanada.
Atiku ya yi kira ga ɓangaren shari’a da ya ci gaba da kare ’yancin jama’a, tabbatar da adalci da kuma mutunta doka domin ƙarfafa dimokuraɗiyya a Nijeriya.














