Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi barazanar shigar da ƙarar neman diyyar Naira biliyan 10 a kan shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual Church, Elijah Ayodele, bisa zargin ɓata masa suna.
Kwankwaso, ta hannun lauyoyinsa na kamfanin Magaji Mato Ibrahim SAN & Co., ya bai wa malamin addinin wa’adin sa’o’i 24 da ya janye kalaman da ake zargin ya yi tare da neman afuwa a bainar jama’a.
A cewar wasiƙar da aka rubuta ranar 11 ga Yuni, 2026, kuma Magaji Mato Ibrahim ya sanya wa hannu, an zargi Primate Ayodele da yin kalamai na ƙarya da ka iya lalata martaba da kimar siyasar Kwankwaso.
Lauyoyin sun ce malamin ya yi kalaman ne yayin wani wa’azi a coci, wanda aka watsa kai tsaye kuma daga baya ya yaɗu a kafafen sada zumunta.
Daga cikin kalaman da aka ce Ayodele ya yi akwai cewa, “Kwankwaso ba amintacce ba ne ga Obi, Kwankwaso zai ci amanar Obi, kuma an biya Kwankwaso kuɗi ne domin ya zama mataimakin shugaban ƙasa ga Obi.”
Lauyoyin Kwankwaso sun bayyana waɗannan kalamai a matsayin cin mutunci da ɓata suna, suna masu cewa suna iya jawo masa asarar mutunci da kuma illa ga matsayinsa na siyasa.
Har zuwa lokacin fitar da wannan rahoto, Elijah Ayodele bai fitar da wata sanarwa a hukumance ba dangane da barazanar shari’ar.














