Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Remi Tinubu, ta yi kira ga matasan Nijeriya da su ɗauki nauyin kula da lafiyarsu ta hanyar yin gwajin cutar ƙanjamau da kuma neman magani, yayin da duniya ke bikin ranar yaƙi da cutar ta ƙanjamau ta 2025.
A cikin wani saƙo da ta fitar a ranar Litinin, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ce; taken na bana shi ne, “Mayar Da Hankali Tare Da Magance Cutar Ƙanjamau,” ya ba da dama ga ƙasar ta hanyar sabunta alƙawarinta na kawo ƙarshen cutar ƙanjamau nan da shekara ta 2030.
Har ila yau, ta yi nuni da cewa; duk da cewa, Nijeriya ta samu ci gaba sosai a fannin rigakafin cutar ƙanjamau da jiyya da kuma kulawa a tsawon shekaru, amma duk da haka akwai buƙatar ƙara yin aiki tuƙuru, don tabbatar da cewa; kowane ɗan ƙasa ya samu damar yin ayyukan ceton rai, ba tare da tsoro ko wariya ba.
- Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
- Sin Na Kokarin Yin Kirkire-kirkire Don Sa Kaimi Ga Samun Moriyar Juna A Duniya
“Kowane ɗan Nijeriya ya cancanci samun damar ceto rai, ba tare da ƙyama ko nuna wariya ba,” in ji ta.
Sanata Tinubu ta buƙaci matasa a faɗin ƙasar nan da su ba da fifiko wajen yin gwaje-gwaje a-kai-a-kai tare da sanar da su game da cutar ƙanjamau.
Har ila yau, ta nanata cewa; gano cutar da wuri da kuma yin magani a kan lokaci na da matuƙar muhimmanci wajen cimma cutar ta ƙanjamau (AIDS).
“Ina kira ga matasanmu, ku kula da lafiyarku, ku san illar cutar HIƁ ta hanyar yin gwaji, sannan kuma ku nemi magani da zarar kun kamu da ita,” in ji ta.
Haka zalika, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta yi kira ga iyalai, masu kulawa da unguwanni da su nuna tausayi tare da bayar da tallafi ga waɗanda ke ɗauke da cutar ta ƙanjamau.
Sannan ta sake nanata cewa, ƙyama na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaba a matakin yaƙi da cutar ta ƙanjamau a faɗin wannan ƙasa, kazalika kuma dole ne a fuskanci juna ta hanyar kawar da wannan ƙyama a tsakanin al’umma.
“Saboda haka, ina kira ga al’umma da ku nuna tausayi da goyon baya tare da kawar da ƙyama a tsakanin masu ɗauke da cutar,” in ji ta.
Sanata Tinubu ta jaddada aniyar gwamnatin tarayya na ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin da ƙasa ke yi na kawo ƙarshen cutar ƙanjamau a matsayin barazana ga lafiyar jama’a nan da shekara ta 2030, wanda hakan ya yi daidai da manufofin duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya da abokan aikin lafiya na duniya ke jagoranta.
Har wa yau, ta ƙarƙare da miƙa fatan alheri ga ɗaukacin ƴan Nijeriya, tana mai cewa, “Barka da ranar Ƙanjamau ta duniya (2025).”














