ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ƙanjamau Ta Duniya: Remi Tinubu Ta Nemi Matasa Su Rungumi Aƙidar Gwaji

by Sani Anwar
6 months ago
Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Remi Tinubu, ta yi kira ga matasan Nijeriya da su ɗauki nauyin kula da lafiyarsu ta hanyar yin gwajin cutar ƙanjamau da kuma neman magani, yayin da duniya ke bikin ranar yaƙi da cutar ta ƙanjamau ta 2025.

A cikin wani saƙo da ta fitar a ranar Litinin, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ce; taken na bana shi ne, “Mayar Da Hankali Tare Da Magance Cutar Ƙanjamau,” ya ba da dama ga ƙasar ta hanyar sabunta alƙawarinta na kawo ƙarshen cutar ƙanjamau nan da shekara ta 2030.

Har ila yau, ta yi nuni da cewa; duk da cewa, Nijeriya ta samu ci gaba sosai a fannin rigakafin cutar ƙanjamau da jiyya da kuma kulawa a tsawon shekaru, amma duk da haka akwai buƙatar ƙara yin aiki tuƙuru, don tabbatar da cewa; kowane ɗan ƙasa ya samu damar yin ayyukan ceton rai, ba tare da tsoro ko wariya ba.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Sin Na Kokarin Yin Kirkire-kirkire Don Sa Kaimi Ga Samun Moriyar Juna A Duniya

“Kowane ɗan Nijeriya ya cancanci samun damar ceto rai, ba tare da ƙyama ko nuna wariya ba,” in ji ta.

Sanata Tinubu ta buƙaci matasa a faɗin ƙasar nan da su ba da fifiko wajen yin gwaje-gwaje a-kai-a-kai tare da sanar da su game da cutar ƙanjamau.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Har ila yau, ta nanata cewa; gano cutar da wuri da kuma yin magani a kan lokaci na da matuƙar muhimmanci wajen cimma cutar ta ƙanjamau (AIDS).

“Ina kira ga matasanmu, ku kula da lafiyarku, ku san illar cutar HIƁ ta hanyar yin gwaji, sannan kuma ku nemi magani da zarar kun kamu da ita,” in ji ta.

Haka zalika, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta yi kira ga iyalai, masu kulawa da unguwanni da su nuna tausayi tare da bayar da tallafi ga waɗanda ke ɗauke da cutar ta ƙanjamau.

Sannan ta sake nanata cewa, ƙyama na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaba a matakin yaƙi da cutar ta ƙanjamau a faɗin wannan ƙasa, kazalika kuma dole ne a fuskanci juna ta hanyar kawar da wannan ƙyama a tsakanin al’umma.

“Saboda haka, ina kira ga al’umma da ku nuna tausayi da goyon baya tare da kawar da ƙyama a tsakanin masu ɗauke da cutar,” in ji ta.

Sanata Tinubu ta jaddada aniyar gwamnatin tarayya na ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin da ƙasa ke yi na kawo ƙarshen cutar ƙanjamau a matsayin barazana ga lafiyar jama’a nan da shekara ta 2030, wanda hakan ya yi daidai da manufofin duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya da abokan aikin lafiya na duniya ke jagoranta.

Har wa yau, ta ƙarƙare da miƙa fatan alheri ga ɗaukacin ƴan Nijeriya, tana mai cewa, “Barka da ranar Ƙanjamau ta duniya (2025).”

Duniya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.