ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ƙanjamau Ta Duniya: Remi Tinubu Ta Nemi Matasa Su Rungumi Aƙidar Gwaji

by Sani Anwar
7 months ago
Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Remi Tinubu, ta yi kira ga matasan Nijeriya da su ɗauki nauyin kula da lafiyarsu ta hanyar yin gwajin cutar ƙanjamau da kuma neman magani, yayin da duniya ke bikin ranar yaƙi da cutar ta ƙanjamau ta 2025.

A cikin wani saƙo da ta fitar a ranar Litinin, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ce; taken na bana shi ne, “Mayar Da Hankali Tare Da Magance Cutar Ƙanjamau,” ya ba da dama ga ƙasar ta hanyar sabunta alƙawarinta na kawo ƙarshen cutar ƙanjamau nan da shekara ta 2030.

Har ila yau, ta yi nuni da cewa; duk da cewa, Nijeriya ta samu ci gaba sosai a fannin rigakafin cutar ƙanjamau da jiyya da kuma kulawa a tsawon shekaru, amma duk da haka akwai buƙatar ƙara yin aiki tuƙuru, don tabbatar da cewa; kowane ɗan ƙasa ya samu damar yin ayyukan ceton rai, ba tare da tsoro ko wariya ba.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Sin Na Kokarin Yin Kirkire-kirkire Don Sa Kaimi Ga Samun Moriyar Juna A Duniya

“Kowane ɗan Nijeriya ya cancanci samun damar ceto rai, ba tare da ƙyama ko nuna wariya ba,” in ji ta.

Sanata Tinubu ta buƙaci matasa a faɗin ƙasar nan da su ba da fifiko wajen yin gwaje-gwaje a-kai-a-kai tare da sanar da su game da cutar ƙanjamau.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

Har ila yau, ta nanata cewa; gano cutar da wuri da kuma yin magani a kan lokaci na da matuƙar muhimmanci wajen cimma cutar ta ƙanjamau (AIDS).

“Ina kira ga matasanmu, ku kula da lafiyarku, ku san illar cutar HIƁ ta hanyar yin gwaji, sannan kuma ku nemi magani da zarar kun kamu da ita,” in ji ta.

Haka zalika, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta yi kira ga iyalai, masu kulawa da unguwanni da su nuna tausayi tare da bayar da tallafi ga waɗanda ke ɗauke da cutar ta ƙanjamau.

Sannan ta sake nanata cewa, ƙyama na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaba a matakin yaƙi da cutar ta ƙanjamau a faɗin wannan ƙasa, kazalika kuma dole ne a fuskanci juna ta hanyar kawar da wannan ƙyama a tsakanin al’umma.

“Saboda haka, ina kira ga al’umma da ku nuna tausayi da goyon baya tare da kawar da ƙyama a tsakanin masu ɗauke da cutar,” in ji ta.

Sanata Tinubu ta jaddada aniyar gwamnatin tarayya na ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin da ƙasa ke yi na kawo ƙarshen cutar ƙanjamau a matsayin barazana ga lafiyar jama’a nan da shekara ta 2030, wanda hakan ya yi daidai da manufofin duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya da abokan aikin lafiya na duniya ke jagoranta.

Har wa yau, ta ƙarƙare da miƙa fatan alheri ga ɗaukacin ƴan Nijeriya, tana mai cewa, “Barka da ranar Ƙanjamau ta duniya (2025).”

Duniya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

MASU ALAKA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.