ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Ƙanjamau Ta Duniya: Remi Tinubu Ta Nemi Matasa Su Rungumi Aƙidar Gwaji

by Sani Anwar
7 months ago
Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Remi Tinubu, ta yi kira ga matasan Nijeriya da su ɗauki nauyin kula da lafiyarsu ta hanyar yin gwajin cutar ƙanjamau da kuma neman magani, yayin da duniya ke bikin ranar yaƙi da cutar ta ƙanjamau ta 2025.

A cikin wani saƙo da ta fitar a ranar Litinin, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ce; taken na bana shi ne, “Mayar Da Hankali Tare Da Magance Cutar Ƙanjamau,” ya ba da dama ga ƙasar ta hanyar sabunta alƙawarinta na kawo ƙarshen cutar ƙanjamau nan da shekara ta 2030.

Har ila yau, ta yi nuni da cewa; duk da cewa, Nijeriya ta samu ci gaba sosai a fannin rigakafin cutar ƙanjamau da jiyya da kuma kulawa a tsawon shekaru, amma duk da haka akwai buƙatar ƙara yin aiki tuƙuru, don tabbatar da cewa; kowane ɗan ƙasa ya samu damar yin ayyukan ceton rai, ba tare da tsoro ko wariya ba.

ADVERTISEMENT
  • Duniya Za Ta Kara Kyau In Ba A Nuna Fin Karfi
  • Sin Na Kokarin Yin Kirkire-kirkire Don Sa Kaimi Ga Samun Moriyar Juna A Duniya

“Kowane ɗan Nijeriya ya cancanci samun damar ceto rai, ba tare da ƙyama ko nuna wariya ba,” in ji ta.

Sanata Tinubu ta buƙaci matasa a faɗin ƙasar nan da su ba da fifiko wajen yin gwaje-gwaje a-kai-a-kai tare da sanar da su game da cutar ƙanjamau.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Har ila yau, ta nanata cewa; gano cutar da wuri da kuma yin magani a kan lokaci na da matuƙar muhimmanci wajen cimma cutar ta ƙanjamau (AIDS).

“Ina kira ga matasanmu, ku kula da lafiyarku, ku san illar cutar HIƁ ta hanyar yin gwaji, sannan kuma ku nemi magani da zarar kun kamu da ita,” in ji ta.

Haka zalika, Uwargidan Shugaban Ƙasar ta yi kira ga iyalai, masu kulawa da unguwanni da su nuna tausayi tare da bayar da tallafi ga waɗanda ke ɗauke da cutar ta ƙanjamau.

Sannan ta sake nanata cewa, ƙyama na ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin manyan abubuwan da ke kawo cikas ga ci gaba a matakin yaƙi da cutar ta ƙanjamau a faɗin wannan ƙasa, kazalika kuma dole ne a fuskanci juna ta hanyar kawar da wannan ƙyama a tsakanin al’umma.

“Saboda haka, ina kira ga al’umma da ku nuna tausayi da goyon baya tare da kawar da ƙyama a tsakanin masu ɗauke da cutar,” in ji ta.

Sanata Tinubu ta jaddada aniyar gwamnatin tarayya na ƙara ƙaimi ga ƙoƙarin da ƙasa ke yi na kawo ƙarshen cutar ƙanjamau a matsayin barazana ga lafiyar jama’a nan da shekara ta 2030, wanda hakan ya yi daidai da manufofin duniya da Majalisar Ɗinkin Duniya da abokan aikin lafiya na duniya ke jagoranta.

Har wa yau, ta ƙarƙare da miƙa fatan alheri ga ɗaukacin ƴan Nijeriya, tana mai cewa, “Barka da ranar Ƙanjamau ta duniya (2025).”

Duniya
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ƴan Ƙwadago Sun Buƙaci Naira 300,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    NiMet Ta Gargaɗi Jihohi 27 Kan Barazanar Ambaliyar Ruwa A Farkon Watan Yuli
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Amince Da Jamilu Gwamna A Matsayin Gwamnan Gombe

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
Next Post
Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Sabon Tsarin Ci Gaban Zamfara Na Shekaru 10

LABARAI MASU NASABA

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.