ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ganin Yanayi Na Tabbas Wajen Tarukan Majalisun Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
3 months ago

Bisa wani rahoton da aka gabatar da shi wajen dandalin tattaunawar tattalin arziki na duniya, an ce yanayin rashin tabbas daya ne daga cikin manyan abubuwan da suke haifar da barazana ga al’ummun kasashe daban daban a shekarar 2026 da muke ciki. Sai dai a nata bangare, kasar Sin tana samar da cikakken yanayi na tabbas, da ake iya ganin alamarsa wajen tarukan shekara-shekara na majalisun NPC da CPPCC, wato hukumar koli ta kafa dokoki da hukumar ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar, dake gudana a birnin Beijing yanzu.

Yanayin tabbas da aka ga alamarsa a tarukan majalisun, da farko dai ya shafi ci gaban tattalin arzikin kasar Sin mai inganci.

A yanzu haka, ’yan majalisun NPC da CPPCC na kasar Sin suna tantance daftarin shirin raya kasar na shekaru 5 masu zuwa, wato tsakanin shekarar 2026 da ta 2030, wanda ya shafi zamanantar da tsarin masana’antu, da inganta kayayyakin more rayuwar jama’a, da raya kimiyya da fasaha, da kirkiro sabbin fasahohi, gami da sauya zuwa salon raya tattalin arziki mai kare muhallin halittu. Wannan shiri ya sa ake hasashen kyakkyawar makomar kasar, musamman ma ta la’akari da kwarewarta ta fuskar aiwatar da shirin da ta tsara, wadda ta tabbatar da karuwar tattalin arzikin kasar ta kaso 5.4% cikin wa’adin shirinta na raya kasa na 2021-2025.

ADVERTISEMENT

Na biyu kuma, yanayi na tabbas da aka gano wajen tarukan majalisun NPC da CPPCC na kasar Sin ya shafi zumuntar da ke tsakanin Sin da Afirka.

A gefen tarukan majalisun NPC da CPPCC na wannan karo, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kira taron manema labaru don ayyana manufofin kasar a fannin harkar diplomasiyya, inda Fortune Abang, wakilin kamfanin dillancin labarai na kasar Najeriya (NAN), ya yi tambaya kan yanayin huldar dake tsakanin Sin da Afirka a shekarar 2026. Yayin da ya amsa tambayar, Wang Yi ya nuna kaunar da Sinawa suke da ita ga abokansu ’yan Afirka, inda ya ambaci al’adar ministan wajen kasar Sin ta mai da nahiyar Afirka wurin kaddamar da ziyara ta farko a duk wata sabuwar shekara, da tarihin kasar Sin na ba da tallafi ga kasashen Afirka, da yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ke dora muhimmanci kan raya huldar dake tsakanin bangarorin 2.

LABARAI MASU NASABA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

Sa’an nan, fanni na 3 da yanayin tabbas da tarukan majalisun NPC da CPPCC suka nuna ya shafa, shi ne yunkurin Sin da Afirka na neman samun ci gaba na bai daya.

Shahararren shehun malami na kasar Najeriya, Charles Onunaiju, ya bayyana a cikin wata makalar da ya rubuta a kwanan nan cewa, yadda kasar Sin ke aiwatar da shirinta na raya kasa zai haifar da dimbin damammakin raya tattalin arziki ga kasashen Afirka, musamman ma ta la’akari da manufar kasar ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka harajin kwastam. Ya ce da manufar, gami da niyyar gwamnatin kasar Sin ta sa kaimi ga bangaren sayayya a cikin gidanta, za a ba kasashen Afirka damar fitar da karin kayayyaki, wanda hakan zai taimaka ga bunkasa masana’antu a kasashen Afirka.

Kana a nasa bangare, wani shehun malami dan kasar Kenya mai suna Stephen Ndegwa, ya bayyana cikin wata makalarsa cewa, kasar Sin ta samu nasara a fannin raya harkar samar da kayayyaki masu fasahohin zamani, wadanda ke taimakawa yunkurin kare muhallin halittu a kasashe daban daban. Hakan ya ba kasashen Afirka da ke da wasu ma’adinai masu muhimmanci a fannin masana’antu masu kare muhalli damar shiga a dama da su, a ayyukan sarrafa ma’adinai, da hada kayayyaki daban daban. (Bello Wang)

CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

MASU ALAKA

Abokin Jibi Shi Ne Aboki
Ra'ayi Riga

Abokin Jibi Shi Ne Aboki

June 3, 2026
Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka
Ra'ayi Riga

Rayukan Mutanen Kenya Na Da Muhimmanci Daidai Da Na ‘Yan Amurka

June 1, 2026
Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya
Ra'ayi Riga

Nagartattun Manufofin Sin Suna Janyo Hankalin Kasashen Duniya

May 29, 2026
Next Post
NDLEA

NDLEA Ta Kama Mutane 56 A Wuraren Hada-hadar Miyagun Ƙwayoyi A Kano

Discussion about this post

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.