ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ana Ganin Yanayi Na Tabbas Wajen Tarukan Majalisun Kasar Sin

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago

Bisa wani rahoton da aka gabatar da shi wajen dandalin tattaunawar tattalin arziki na duniya, an ce yanayin rashin tabbas daya ne daga cikin manyan abubuwan da suke haifar da barazana ga al’ummun kasashe daban daban a shekarar 2026 da muke ciki. Sai dai a nata bangare, kasar Sin tana samar da cikakken yanayi na tabbas, da ake iya ganin alamarsa wajen tarukan shekara-shekara na majalisun NPC da CPPCC, wato hukumar koli ta kafa dokoki da hukumar ba da shawara kan harkokin siyasa na kasar, dake gudana a birnin Beijing yanzu.

Yanayin tabbas da aka ga alamarsa a tarukan majalisun, da farko dai ya shafi ci gaban tattalin arzikin kasar Sin mai inganci.

A yanzu haka, ’yan majalisun NPC da CPPCC na kasar Sin suna tantance daftarin shirin raya kasar na shekaru 5 masu zuwa, wato tsakanin shekarar 2026 da ta 2030, wanda ya shafi zamanantar da tsarin masana’antu, da inganta kayayyakin more rayuwar jama’a, da raya kimiyya da fasaha, da kirkiro sabbin fasahohi, gami da sauya zuwa salon raya tattalin arziki mai kare muhallin halittu. Wannan shiri ya sa ake hasashen kyakkyawar makomar kasar, musamman ma ta la’akari da kwarewarta ta fuskar aiwatar da shirin da ta tsara, wadda ta tabbatar da karuwar tattalin arzikin kasar ta kaso 5.4% cikin wa’adin shirinta na raya kasa na 2021-2025.

ADVERTISEMENT

Na biyu kuma, yanayi na tabbas da aka gano wajen tarukan majalisun NPC da CPPCC na kasar Sin ya shafi zumuntar da ke tsakanin Sin da Afirka.

A gefen tarukan majalisun NPC da CPPCC na wannan karo, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya kira taron manema labaru don ayyana manufofin kasar a fannin harkar diplomasiyya, inda Fortune Abang, wakilin kamfanin dillancin labarai na kasar Najeriya (NAN), ya yi tambaya kan yanayin huldar dake tsakanin Sin da Afirka a shekarar 2026. Yayin da ya amsa tambayar, Wang Yi ya nuna kaunar da Sinawa suke da ita ga abokansu ’yan Afirka, inda ya ambaci al’adar ministan wajen kasar Sin ta mai da nahiyar Afirka wurin kaddamar da ziyara ta farko a duk wata sabuwar shekara, da tarihin kasar Sin na ba da tallafi ga kasashen Afirka, da yadda shugaban kasar Sin Xi Jinping ke dora muhimmanci kan raya huldar dake tsakanin bangarorin 2.

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Sa’an nan, fanni na 3 da yanayin tabbas da tarukan majalisun NPC da CPPCC suka nuna ya shafa, shi ne yunkurin Sin da Afirka na neman samun ci gaba na bai daya.

Shahararren shehun malami na kasar Najeriya, Charles Onunaiju, ya bayyana a cikin wata makalar da ya rubuta a kwanan nan cewa, yadda kasar Sin ke aiwatar da shirinta na raya kasa zai haifar da dimbin damammakin raya tattalin arziki ga kasashen Afirka, musamman ma ta la’akari da manufar kasar ta yafe wa kasashe 53 dake nahiyar Afirka harajin kwastam. Ya ce da manufar, gami da niyyar gwamnatin kasar Sin ta sa kaimi ga bangaren sayayya a cikin gidanta, za a ba kasashen Afirka damar fitar da karin kayayyaki, wanda hakan zai taimaka ga bunkasa masana’antu a kasashen Afirka.

Kana a nasa bangare, wani shehun malami dan kasar Kenya mai suna Stephen Ndegwa, ya bayyana cikin wata makalarsa cewa, kasar Sin ta samu nasara a fannin raya harkar samar da kayayyaki masu fasahohin zamani, wadanda ke taimakawa yunkurin kare muhallin halittu a kasashe daban daban. Hakan ya ba kasashen Afirka da ke da wasu ma’adinai masu muhimmanci a fannin masana’antu masu kare muhalli damar shiga a dama da su, a ayyukan sarrafa ma’adinai, da hada kayayyaki daban daban. (Bello Wang)

CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Kungiyar Hadin Gwiwar Fasahar AI Ta Duniya A Shanghai
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya
  • Sulaiman
    Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara
  • Sulaiman
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

MASU ALAKA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI
Ra'ayi Riga

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Next Post
NDLEA

NDLEA Ta Kama Mutane 56 A Wuraren Hada-hadar Miyagun Ƙwayoyi A Kano

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.