Aƙalla mutum takwas, ciki har da wani ɗalibin Amin ƙarshe (Level 400) na Jami’ar Tarayya ta Dutsin-Ma (FUDMA), Ibrahim Danbaba, da yara huɗu, sun mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya afku a hanyar Funtua zuwa Katsina, a Layin Kukah da ke Ƙaramar Hukumar Bakori ta Jihar Katsina. Wasu mutum 17 kuma sun samu raunuka daban-daban.
Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC) reshen Jihar Katsina ta ce hatsarin ya faru da misalin ƙarfe 1:32 na rana a ranar Lahadi. Hatsarin ya rutsa da motar bas kirar Toyota Hiace mai lambar rajista 14B 92 TR da kuma babur mai kafa uku (Keke Napep) kirar Bajaj wanda ba shi da lambar rajista.
Jami’in wayar da kan Jama’a na FRSC a jihar, DRC Shamsudeen Babajo, ya ce mutum 25 ne hatsarin ya rutsa da su. Daga cikinsu, mutum 17 sun samu raunuka da suka haɗa da karaya da munanan yanke-yanke, yayin da mutum takwas suka rasu. Ya kuma bayyana cewa babu ko mutum ɗaya da ya tsira ba tare da rauni ba.
Binciken farko na hukumar ya nuna cewa yin gudun wuce gona da iri da ƙin ƙa’ida ne ya haddasa hatsarin. Tawagar ceto ta FRSC tare da haɗin gwiwar Community Watch Corps (C-Watch) sun kai ɗauki, inda aka garzaya da waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Bakori Comprehensive domin samun kulawa, sannan aka kai gawarwakin mamatan zuwa Babban Asibitin Funtua.














