Gwagwarmayar neman kujerun Majalisar Dokokin Jihar Kwara ta ƙara ɗaukar zafi a ranar Litinin yayin da jam’iyyar APC ta fara tantance masu neman takara domin samun tikitin kujeru 24 na majalisar a faɗin jihar.
Jimillar masu neman takara 158 ne ke fafatawa domin samun tikitin jam’iyyar, lamarin da ke nuna cewa, za a yi gwagwarmaya mai zafi kafin zaɓe mai zuwa.
Shugaban kwamitin tantancewar, Farfesa Success Jubril Musa, ne ya bayyana adadin yayin gudanar da aikin a sakatariyar APC da ke Ilorin.
Ya tabbatar wa masu neman takarar cewa za a gudanar da aikin cikin gaskiya da adalci ba tare da nuna son kai ba.Ya ce an zaɓi mambobin kwamitin ne bisa gaskiya da ƙwarewa da kuma mutunci.
Musa ya jaddada cewa adalci zai kasance babban ginshiƙin da za a bi wajen gudanar da tantancewar.















Discussion about this post