Kasar Sin ta bayar da rahoton samun karuwar jami’an jinya da kashi 29 cikin dari a tsakanin shekarar 2020 zuwa 2025, inda adadinsu ya haura miliyan 6.06 zuwa karshen bara, kamar yadda hukumar kula da kiwon lafiya ta kasa (NHC) ta bayyana a yau Litinin.
A cewar bayanan hukumar ta NHC, adadin jami’an jinya da aka yi wa rajista a kan mizanin kowane jami’i ya kula da mutum 1000, ya karu daga kashi 3.34 a shekarar 2020 zuwa kaso 4.32 a 2025.
Kana, fiye da kashi 80 cikin 100 na jami’an sun mallaki takardun kammala karatu ko dai na kwaleji ko na gaba da ita.A cikin shirinta na bunkasa ci gaban kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15 (daga 2026 zuwa 2030), kasar Sin ta kuduri aniyar hanzarta samun ci gaba a muradunta na gina ingantaccen tsarin kiwon lafiya da zai shafi kowa da kowa a kasar nan da shekarar 2035.
Shirin ya yi kiran samar da ayyukan kiwon lafiya mai adalci da kuma kyakkyawan tsari ga al’umma domin bunkasa kiwon lafiyar jama’a baki daya. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)















Discussion about this post