ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

APC Da NNPP Sun Lashe Zaɓen Cike Gurbi Na Majalisar Dokokin Kano

by Sulaiman
10 months ago
NNPP

Jam’iyyar NNPP da APC sun samu nasara a zaɓen cike gurbi na jihar Kano da aka gudanar a ranar Asabar.

 

Da yake sanar da sakamakon da misalin karfe 12:36 na daren Lahadi, Jami’in zaɓe na hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC), mai kula da mazaɓar Bagwai/Shanono, Farfesa Hassan Adamu Shitu, ya bayyana dan takarar jam’iyyar NNPP, Dr. Ali Hassan Kiyawa a matsayin wanda ya lashe zaɓen da kuri’u 16,198 kan Ahmad Muhammad Kadamu na APC, wanda ya samu kuri’u 5,347.

ADVERTISEMENT
  • Me Ya Sa Ciwon ACL Ya Zama Barazana Ga ‘Yan Wasan Kwallo?
  • Zaɓen Cike Gurbi: Jauro APC Ne Ya Lashe Kujerar Ganye Ta Adamawa – INEC

Har ila yau, da misalin karfe 6:10 na safiyar Lahadi, jami’in zaɓe na INEC mai wakiltar Ghari/Tsanyawa, Farfesa Muhammad Waziri, ya bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Garba Ya’u Gwarmai a matsayin wanda ya lashe zaɓen da kuri’u 31,472 inda ya doke Yusuf Ali Maigado na NNPP, wanda ya samu kuri’u 27,931.

 

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

An gudanar da zaɓen ne bayan da INEC ta ayyana zaɓen a baya a matsayin wanda bai kammalu ba.

 

LEADERSHIP ta ruwaito a ranar Asabar cewa, jam’iyyar APC ta yi watsi da yadda zaɓen ya gudana, inda ta bukaci a soke zaɓukan biyu bisa zargin tayar da tarzoma daga ayyukan ‘yan daba.

 

Kiran ya sa shugabannin NNPP suka gudanar da zaman dirshan a ofishin tattara sakamakon zaɓen, inda suka zargi hukumar da yunkurin yin magudi a mazaɓar Ghari/Tsanyawa.

 

Mai magana da yawun gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa wanda ke cikin shugabannin NNPP, ya tabbatar da cewa ‘ya’yan jam’iyyar ba za su fice daga cibiyar tattara sakamakon zaɓen ba har sai an bayyana sakamakon a hukumance.

NNPP
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai
  • Sulaiman
    2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna
  • Sulaiman
    Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

June 10, 2026
Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya
Manyan Labarai

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru
Manyan Labarai

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Mijina Da ’Ya’yana 4 A Lokaci Ɗaya — Bazawara

June 10, 2026
Next Post
Tattakin Arba’in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

Tattakin Arba'in: Muna Farin Ciki Da Yadda Gwamnati Ta Fahimci Ayyukan Mu Na Addini – Ahlul-Baiti

LABARAI MASU NASABA

Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

Kano: Hisbah Ta Tantance Mutane 720 Waɗanda Za A Yi Wa Auren Gata

June 10, 2026
Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

Kotu Ta Bayar Da Umarnin Kamo Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi Na NDC, Ibrahim Kashim

June 10, 2026
Gwamnatin Jigawa Ta Dage Komawa Makaranta Saboda Kidayar Jama’a

‘Yansanda Sun Kama Masu Satar Mutane, ‘Yan Fashi A Jigawa, Sun Ƙwato Makamai

June 10, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

‘Yan Bindiga Sun Yi Kwanton-Ɓauna, Sun Kashe Sojoji 7 A Kaduna

June 10, 2026
Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

Hauhawar Farashi Da Rashin Tsaro Ne Manyan Ƙalubalen Nijeriya — Gwamnatin Tarayya

June 10, 2026
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

Yadda ‘Yan Bindiga Suka Kashe Mijina Da ’Ya’yana 4 A Lokaci Ɗaya — Bazawara

June 10, 2026
Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

Wang Yi Ya Bukaci A Inganta Fahimtar Juna Ta Hanyar Tattaunawa Tsakanin Mabambantan Wayewar Kai

June 9, 2026
ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

Bangaren Sin Ya Yi Kira Da a Dukufa Wajen Neman Mafita Ta Siyasa A Rikicin Ukraine

June 9, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’in Tsaro, Sun Yi Garkuwa Da Mutane Da Dama A Sokoto

June 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.